Leadership News Hausa:
2025-09-17@23:13:17 GMT

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (2)

Published: 23rd, May 2025 GMT

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (2)

A gefe guda kuma, al’ummar yankin ne suka sadaukar da gonakinsu, domin amfanin jama’a wajen gina sansanin FCDA. An cimma yarjejeniya cewa; a karshen amfani da filin, za a mayar da shi ga al’umma. Malam Ladan, ya dage har aka tabbatar da wannan yarjejeniya a rubuce kuma Marigayi Abubakar Koko, Sakataren FCDA, ya sa hannu don kada a samu sabanin tarihi.

Amma duk da haka, ba a mika kadarar ba har zuwa shekarar 1987, bayan fafutukar kwato ta tsawon lokaci. Daga bisani kuma, aka mika ta ga kungiyar tsoffin sojoji ta Nijeriya (Nigerian Legion), bayan sun nemi haka. Abin bakin ciki, gwamnatin tarayya ta kara lissafa filin a matsayin daya daga cikin kadarorinta da za a sayar a zamanin mulkin Obasanjo.

Da ba a gano takardun da Marigayi Koko ya sa hannu a kansu daga cikin tsohuwar ajiyar Jihar Neja ba, da an kwace filin. Wannan kuwa sakamakon hangen nesa ne na Malam Ladan.

Bayan dawo da ikon filin a karo na biyu a ranar 30 ga Oktoba, 2007, al’umma suka mika filin ga Gwamnatin Jihar Neja, domin bai wa Jami’ar IBB ta jihar damar kafa reshe a Suleja. Amma fiye da shekara 17 da yin haka, Gwamnatin Neja ta kasa ware ko sisin kwabo don fara gina wannan reshe.

Abin takaici, tun bayan kirkiro Jihar Neja a 1975, babu wata jami’ar gaba da sakandire da gwamnatin jiha ko ta tarayya ta kafa a Masarautar Suleja, duk da koke-koke da dama, har ma da kiran da dan Majalisar Suleja ya yi kwanan nan a gaban majalisar jihar. Wasu sassan na jihar har suna alfahari da dama daga cikin irin wadannan cibiyoyi. Har da shirin kafa makarantar koyon aikin jinya a tsohon wurin makarantar jinya ta FCT a sansanin FCDA ya zama kawai na cin fuska ne kawai. Hakan na faruwa duk da cewa; akwai Cibiyar Lafiya ta Tarayya da aka ware domin Suleja, amma aka karkatar da ita zuwa wani gari a cikin jihar.

Yankin Masarautar Suleja, shi ne mafi tasiri a fannin tattalin arziki a Jihar Neja, saboda kusancinsa da babban birnin tarayya. Gwamnatin Jihar Neja, na ci gaba da cin moriyar hakan ta hanyar tara haraji masu tarin yawa kamar PAYE, kudin filaye da kadarori da sauran haraji. Masarautar Suleja ita kadai na ba da akalla kashi 40 cikin 100 na kudaden da jihar ke samu daga cikin gida. Kudaden harajin da ake tarawa daga Karamar Hukumar Suleja, sun fi na kowace karamar hukuma a jihar. A kwana-kwanan nan, gwamnan ya bayyana haka.

Amma fa, idan aka kwatanta da wasu garuruwa a cikin jihar, ingancin titin da ake ginawa a cikin birnin Suleja, bai kai kima ba ko kadan. Daga Maje zuwa Madalla, ana iya cewa kwangila ce ta biliyoyin Nairori. Amma kuma, babu wani allon kwangila da ke bayyana sunan dan kwangilar ko hukumar da ke sa ido. Wannan yana nuna irin gazawar da ake da ita wajen gaskiya da rikon amana cikin mulki.

Jama’ar Suleja da masu kaunar garin, ba su da wani zabin da ya wuce su saka a ransu cewa; wata boyayyar makarkashiya ce aka shirya, don rage kudin aikin domin amfanuwar wasu. Wannan kuwa, wata shaida ce ta yadda ake yi wa wanda ke kawo riba wulakanci. Abin takaici ne a ce garin da ke bayar da kudaden shiga ya zama wanda aka watsar da shi a fannin gine-gine da walwalar jama’a.

Za a ci gaba In Shaa Allah.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe

Ƙungiyar shugabannin ƙananan hukumomin Jihar Yobe (ALGON) ta karrama Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, da lambar yabo ta karramawa bisa himmar ayyukan raya ƙasa da gwamnatinsa ke gudanarwa a faɗin jihar.

Karramawar, wacce aka bayyana a matsayin irinta ta farko a tarihin Jihar Yobe, shugabannin ƙananan hukumomi 17 na jihar suka ba da ita ga gwamna.

Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno

Da yake jawabi, shugaban ƙungiyar ALGON a Jihar Yobe, kuma shugaban ƙaramar hukumar Damaturu, Alhaji Bukar Adamu, ya yaba da yadda Gwamna Buni yake gudanar da harkokin mulki na bai ɗaya. Ya ce nasarorin da aka samu sun haɗa da fannoni na ilimi, noma, kiwon lafiya, kasuwanci, da samar da ababen more rayuwa.

“Babu wani sashe a jihar da aka bari a baya a cikin ayyukan ci gaban da Gwamna Mai Mala Buni ke aiwatarwa,” in ji Adamu.

A nasa martanin, Gwamna Buni, wanda mataimakinsa, Alhaji Idi Barde Gubana, ya wakilta, ya karɓi karramawar a matsayin “hanyar mayar da martani mai ƙarfi” da ke tabbatar da tasirin gwamnatinsa a matakin farko.

Ya kuma yi alƙawarin ci gaba da ƙoƙarin kai Yobe matsayin jiha da za ta iya gogayya da takwarorinta a fagen ci gaban ƙasa.

Wakilinmu ya ruwaito cewa taron ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, ’yan siyasa daga ciki da wajen jihar, da kuma sarakunan gargajiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • Tinubu ya janye dokar ta-ɓaci da ya sanya a Ribas
  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
  • NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar
  • Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan Neja
  • An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin