Onyemekara ya sanar da cewa, rahoton na karya da kafar yada labaran ta wallafa kan zargin cin hancin na biliyoyin Naira, na kanzon Kurege ne, wanda kuma bai da wata tushe, ballantana wata makama.

Kazalika, ya bayar da tabbacin cewa, NPA kamar yadda ta saba, za ta ci gaba da gudanar da ayyukanta bisa gaskiya da rikon amana, musamman kan abinda ya shafi, ayyukan kashe kudade.

Onyemekara ya kuma yi watsi da batun zargin badakalar hada-hada a ofishin Hukumar NPA da ke a Birtaniya, inda ya sanar da cewa, babu wani batun wata hada-hadar ayyuka a ofishin makamancin haka, da aka gudanar a ofishin.

Ya yi kira ga kafafen yada labarai na kasar nan, da su tabbatar da suna tuntubar Hukumar kan duk wani rahoton da suke son wallafawa, musamman duba da cewa, kofar Hukumar ako da yaushe bude take, domin yin duk wata suka, mai ma’ana.

Ya sanar da cewa, a karkashin Shugabancin Shugaban Hukumar Abubakar Dantsoho, ya mayar da hankali wajen ganin an zamanantar da ayyukan NPA, musamman ta hanyar samar da kayan aiki, da kuma kara gyara sauran kayan da NPA ke amfani da su.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu

Shugaba Bola Tinubu ya mayar wa da Shugaban Amurka, Donald Trump martani cewa Najeriya ba ta yadda da duk wani nau’in zarafin addini.

Tinubu, ya yi wannan bayani ne bayan Trump ya sake sanya Najeriya cikin jerin ƙasashen da ake kiran “Ƙasashen da ke da Babbar Matsala wajen ’Yancin Addini.”

PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu ’yan tsagin Wike Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa

Trump ya yi iƙirarin cewa Kiristoci a Najeriya na fuskantar barazana, amma ya sha alwashin cewa Amurka za ta kare su.

A cikin wani saƙo da ya wallafa a kafafen sada zumunta, Trump ya rubuta cewa: “Addinin Kirista yana fuskantar babbar barazana a Najeriya. Ana kashe dubban Kiristoci.”

A ranar Asabar, Tinubu ya mayar da martani ta kafar sada zumunta, inda ya ce Najeriya ƙasa ce mai dimokuraɗiyya wadda kundinta ya tabbatar da ’yancin yin addini.

“Najeriya tana da cikakken tanadi a kundinta da ya tabbatar da ’yancin yin addini,” in ji Tinubu.

“Tun daga shekarar 2023, gwamnatina na aiki tare da shugabannin Kiristoci da Musulmai don magance matsalolin tsaro da ke shafar jama’a daga kowane ɓangare da addini.”

Ya ƙara da cewa, kiran Najeriya ƙasa mai matsala wajen gudanar addini ba gaskiya ba ne.

“Za mu ci gaba da kare ’yancin kowane ɗan ƙasa na yin addininsa cikin walwala. Najeriya ba ta goyon bayan zaluncin addini ko kaɗan,” in ji Tinubu.

Ya kuma ce Najeriya za ta ci gaba da haɗa kai da Amurka da sauran ƙasashe domin inganta zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin mabiya addinai daban-daban.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa
  • IAEA : Babu wata shaida da ke nuna cewa Iran na kera makaman nukiliya
  • Tinubu zai gana da Trump kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya 
  • Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu
  • Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa
  • Israila Ta Kai Hari  Kan Ofishin kungiyar UNICEF Dake Gaza A
  • Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace
  • M D Duniya Tayi Gargadi Game Da Gwajin Nukiliya Da Amurka Ta Sanar Za ta yi
  • NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa
  • Madagascar Ta Sanar da Kafa Sabuwar Gwamnati Tare da Manyan ‘Yan Adawa