Onyemekara ya sanar da cewa, rahoton na karya da kafar yada labaran ta wallafa kan zargin cin hancin na biliyoyin Naira, na kanzon Kurege ne, wanda kuma bai da wata tushe, ballantana wata makama.

Kazalika, ya bayar da tabbacin cewa, NPA kamar yadda ta saba, za ta ci gaba da gudanar da ayyukanta bisa gaskiya da rikon amana, musamman kan abinda ya shafi, ayyukan kashe kudade.

Onyemekara ya kuma yi watsi da batun zargin badakalar hada-hada a ofishin Hukumar NPA da ke a Birtaniya, inda ya sanar da cewa, babu wani batun wata hada-hadar ayyuka a ofishin makamancin haka, da aka gudanar a ofishin.

Ya yi kira ga kafafen yada labarai na kasar nan, da su tabbatar da suna tuntubar Hukumar kan duk wani rahoton da suke son wallafawa, musamman duba da cewa, kofar Hukumar ako da yaushe bude take, domin yin duk wata suka, mai ma’ana.

Ya sanar da cewa, a karkashin Shugabancin Shugaban Hukumar Abubakar Dantsoho, ya mayar da hankali wajen ganin an zamanantar da ayyukan NPA, musamman ta hanyar samar da kayan aiki, da kuma kara gyara sauran kayan da NPA ke amfani da su.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Gamsu Da Lokaci Da Wurin Da Za A Gudanar Da Shawarwarinta Da Amurka Zagaye Na Biyar

Iran ta sanar da lokaci da kuma wurin da za a yi sabon shawarwari tsakanin Iran da Amurka

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya sanar da cewa: A gobe Juma’a ne za a gudanar da zagaye na biyar na shawarwari tsakanin Iran da Amurka a birnin Roma.

A lokacin da ya isa birnin Shiraz don halartar taron yankin kan harkokin diflomasiyya na cikin gida, Araghchi ya bayyana cewa, gudanar da wannan taro da ya fi mayar da hankali kan diflomasiyyar tattalin arzikin yankin, ya shiga cikin tsarin manufofin makwabtaka na Iran, yana mai jaddada cewa, ko shakka babu za ta yi tasiri.

Araqchi ya kara da cewa “Za a gudanar da tattaunawar zagaye na biyar ranar Juma’a a Roma babban birnin Italiya.”

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Isma’il Baqa’i a cikin wata sanarwa da ya fitar ya yi nuni da shawarar da masarautar Oman ta gabatar da kuma tuntubar da take gudanarwa na gudanar da wani sabon zagaye na shawarwari tsakanin Iran da Amurka a gobe Juma’a a birnin Roma na kasar Italiya, inda ya sanar da amincewar Jamhuriyar Musulunci ta Iran da wannan shawara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • El-Rufai Ya Zargi Bangaren Shari’a Da Cin Hanci Da Rashawa
  • Allah Ya Isa: Shugaban PDP Damagun ya musanta zargin yi wa APC aiki
  • Iran Ta Gamsu Da Lokaci Da Wurin Da Za A Gudanar Da Shawarwarinta Da Amurka Zagaye Na Biyar
  • Wani Mutum Ya Harbe Ma’aikatan Ofishin Jakadancin Isra’ila A Birnin Washington Na Amurka
  • Gwamnatin Afirka Ta Kudu Ta Musanta Zargin Cin Zarafin Turawa ‘Yan Kasar Fararen Fata
  • Ma’aikatan Wutar Lantarki A Katsina Sun Tsunduma Yajin Aiki
  • Rukunin Karshe Na Alhazan Jigawa Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
  • Hukumar tace fina-finai ta soke lasisin gidajen gala 8 a Kano
  • Wani Mutum Ya Kashe Matarsa Da Duka Har Lahira A Edo