Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata
Published: 24th, May 2025 GMT
Onyemekara ya sanar da cewa, rahoton na karya da kafar yada labaran ta wallafa kan zargin cin hancin na biliyoyin Naira, na kanzon Kurege ne, wanda kuma bai da wata tushe, ballantana wata makama.
Kazalika, ya bayar da tabbacin cewa, NPA kamar yadda ta saba, za ta ci gaba da gudanar da ayyukanta bisa gaskiya da rikon amana, musamman kan abinda ya shafi, ayyukan kashe kudade.
Onyemekara ya kuma yi watsi da batun zargin badakalar hada-hada a ofishin Hukumar NPA da ke a Birtaniya, inda ya sanar da cewa, babu wani batun wata hada-hadar ayyuka a ofishin makamancin haka, da aka gudanar a ofishin.
Ya yi kira ga kafafen yada labarai na kasar nan, da su tabbatar da suna tuntubar Hukumar kan duk wani rahoton da suke son wallafawa, musamman duba da cewa, kofar Hukumar ako da yaushe bude take, domin yin duk wata suka, mai ma’ana.
Ya sanar da cewa, a karkashin Shugabancin Shugaban Hukumar Abubakar Dantsoho, ya mayar da hankali wajen ganin an zamanantar da ayyukan NPA, musamman ta hanyar samar da kayan aiki, da kuma kara gyara sauran kayan da NPA ke amfani da su.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Gamsu Da Lokaci Da Wurin Da Za A Gudanar Da Shawarwarinta Da Amurka Zagaye Na Biyar
Iran ta sanar da lokaci da kuma wurin da za a yi sabon shawarwari tsakanin Iran da Amurka
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya sanar da cewa: A gobe Juma’a ne za a gudanar da zagaye na biyar na shawarwari tsakanin Iran da Amurka a birnin Roma.
A lokacin da ya isa birnin Shiraz don halartar taron yankin kan harkokin diflomasiyya na cikin gida, Araghchi ya bayyana cewa, gudanar da wannan taro da ya fi mayar da hankali kan diflomasiyyar tattalin arzikin yankin, ya shiga cikin tsarin manufofin makwabtaka na Iran, yana mai jaddada cewa, ko shakka babu za ta yi tasiri.
Araqchi ya kara da cewa “Za a gudanar da tattaunawar zagaye na biyar ranar Juma’a a Roma babban birnin Italiya.”
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Isma’il Baqa’i a cikin wata sanarwa da ya fitar ya yi nuni da shawarar da masarautar Oman ta gabatar da kuma tuntubar da take gudanarwa na gudanar da wani sabon zagaye na shawarwari tsakanin Iran da Amurka a gobe Juma’a a birnin Roma na kasar Italiya, inda ya sanar da amincewar Jamhuriyar Musulunci ta Iran da wannan shawara.