Tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Babachir Lawal, ya ce goyon bayan da wasu gwamnonin APC suka nuna wa Shugaba Bola Tinubu domin ya sake tsayawa takara a 2027 bai dame su ba.

Ya ce su a cikin ƙungiyarsu ta masu haɗaka sun fi mayar da hankali ne kan talakawa, ba shugabanni ba.

Gwamnatin Gombe za ta taimaki ’yar shekara 14 da aka yi wa auren dole Ndume ya jinjina wa Tinubu kan bai wa ’yan Arewa sabbin muƙamai

“Ko da dukkanin gwamnonin jihohi 36 da Abuja sun koma APC, babu abin da zai canja.

“Su da danginsu ba su fi ƙuri’u 1000 ba. Abin da muke so shi ne jama’a,” in ji Lawal a hirarsa da jaridar Nigerian Tribune.

Ƙungiyar masu haɗaka ƙarƙashin jagorancin Atiku Abubakar, Peter Obi, da Nasir El-Rufai ta zaɓi jam’iyyar ADC a matsayin jam’iyyar da za su kara da APC a zaɓen 2027.

“Mun ƙudiri niyya sosai. Muna da ƙwarewa kuma muna aiki a hankali. A lokacin da ya dace ne za mu bayyana wa duniya shirinmu,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: adawa Gwamnoni Haɗaka

এছাড়াও পড়ুন:

Kotu ta bai wa EFCC izinin binciken sayar da filin musabaƙar Alƙur’ani na N3.5bn a Kano

Babbar Kotun Tarayya da ke Jihar Kano, ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a S.M. Shuaibu ta ƙi amincewa da buƙatar wasu mambobin Kwamitin Musabaƙar Alƙur’ani da ke son a hana EFCC bincike kan yadda aka sayar da wani fili mai darajar Naira biliyan 3.5.

Filin da ake magana a kai yana bayan titin Ahmadu Bello Way, kuma yana da faɗin hekta biyu.

Sojoji sun kashe mayaƙan ISWAP 16 a Borno An kama jami’in Hukumar NRC da laifin satar waya

Tsohon Gwamnan Sojan Kano, Kanal Abdullahi Wase ne, ya bayar da filin don a gina katafaren waje da za a riƙa gudanar da musabaƙar Alƙur’ani duk shekara.

Amma daga baya sai wasu mambobin kwamitin suka ga an gina gidaje 38 a filin ba tare da sanin su ba.

Hakan ne ya sa a ranar 11 ga watan Nuwamba, 2023, wasu daga cikin amintattun kwamitin suka kai wa EFCC ƙara, domin ta binciki yadda aka sayar da filin a ɓoye.

Waɗanda suka shigar da ƙarar sun haɗa da Sheikh Ibrahim Shehu Mai Hula, Sheikh Gwani Yahuza Danzarga, Tijjani Bala Kalarawi, Aliyu Harazimi, Barrister Saidu Koki, Ado Shehu Maibargo, Dokta Aliyu Darma, Tijjani Mai Lafiya Sanka, Alhaji Tukur Gadanya da Alhaji Sabiu Bako.

Sun buƙaci kotu ta hana EFCC gayyatarsu ko cafke su dangane da wannan batu, sun dogar da wasu sashe na kundin tsarin mulki da yarjejeniyar kare haƙƙin ɗan adam ta Afirka.

Amma kotu ta ce EFCC na da hurumin gudanar da bincike kamar yadda doka ta tanadar, kuma babu kotun da za ta hana hakan, musamman idan ana zargin aikata laifi.

Don haka, kotu ta bayyana cewa waɗana ake ƙara su biya Naira 250,000 ga waɗanda suka yi ƙararsu, saboda ɓata musu lokaci.

Lauyoyin da suka kare wanda ake ƙara – Sadiq Yahya da John Chukwu Eze – sun yaba da hukuncin kotun, yayin da lauyan masu ƙara, Yahaya Isa Abdulrasheed, ya ce za su ɗaukaka ƙara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Warware Basussuka: WAEC DA NECO Sun Saki Sakamakon Ɗaliban Zamfara Na Shekara Biyar
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi
  • Kungiyar Ta’addanci Ta ISIS Ta Zargi Shugaban Gwamnatin Siriya Da Kauce Hanya Madaidaiciya
  • Kotu ta bai wa EFCC izinin binciken sayar da filin musabaƙar Alƙur’ani na N3.5bn a Kano
  • 2027: ’Yan Najeriya sun yi watsi da takarar Tinubu, sun koka kan tsadar rayuwa
  • Jam’iyyar APC A Najeriya Ta Tabbatar Da Tinubu A Matsayin Dan Takarar Shugaban Kasa A Jam’iyyar A Shekara Ta 2027
  • Ba mu tilasta wa kowa ya koma APC ba – Tinubu
  • Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 
  • Ƙungiyar ’yan Majalisar Dokokin Ƙasa Ta APC Ta Amince Da Takarar Tinubu A Zaɓen 2027