Tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Babachir Lawal, ya ce goyon bayan da wasu gwamnonin APC suka nuna wa Shugaba Bola Tinubu domin ya sake tsayawa takara a 2027 bai dame su ba.

Ya ce su a cikin ƙungiyarsu ta masu haɗaka sun fi mayar da hankali ne kan talakawa, ba shugabanni ba.

Gwamnatin Gombe za ta taimaki ’yar shekara 14 da aka yi wa auren dole Ndume ya jinjina wa Tinubu kan bai wa ’yan Arewa sabbin muƙamai

“Ko da dukkanin gwamnonin jihohi 36 da Abuja sun koma APC, babu abin da zai canja.

“Su da danginsu ba su fi ƙuri’u 1000 ba. Abin da muke so shi ne jama’a,” in ji Lawal a hirarsa da jaridar Nigerian Tribune.

Ƙungiyar masu haɗaka ƙarƙashin jagorancin Atiku Abubakar, Peter Obi, da Nasir El-Rufai ta zaɓi jam’iyyar ADC a matsayin jam’iyyar da za su kara da APC a zaɓen 2027.

“Mun ƙudiri niyya sosai. Muna da ƙwarewa kuma muna aiki a hankali. A lokacin da ya dace ne za mu bayyana wa duniya shirinmu,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: adawa Gwamnoni Haɗaka

এছাড়াও পড়ুন:

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima
  • Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo
  • Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani
  • Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
  • DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu
  • DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar
  • Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago
  • An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin