An kaddamar da wani sabon babban filin wasa a birnin N’Djamena na kasar Chadi, wanda kasar Sin ta gina wa kasar kyauta.

Yayin bikin kaddamarwar da ya gudana ranar Juma’a, shugaban kasar Chadi Mahamat Idriss Deby, ya buga kwallon kafa da kansa, a matsayin alamar fara amfani da babban filin wasan.

Cikin jawabin da ya gabatar, shugaba Deby ya gode wa kasar Sin, gami da bayyana filin wasan a matsayin daya daga cikin sakamakon da aka cimma, bisa huldar hadin kai, da mutunta juna, da ta kasance tsakanin kasashen Chadi da Sin.

Wani kamfanin kasar Sin ne ya gina babban filin wasan tare da mika shi ga kasar Chadi a ranar 12 ga wata. Girman filin wasan ya kai muraba’in mita dubu 33, wanda ya kunshi kujerun masu kallon wasanni dubu 30, da filayen wasan kwallon kafa, da na kwallon kwando, da dimbin na’urorin zamani daban daban. (Bello Wang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: filin wasan kasar Chadi

এছাড়াও পড়ুন:

Fiye Da Mata 300 Ne Cikinsu Ya Zube Saboda  Rashin Abinci Mai Gina Jiki A Gaza

Ofishin watsa labaru na hukuma a Gaza ya yi kira ga kungiyoyin kasa da kasa da kuma kungiyoyin jin kai, da su yi aiki da nauyin da ya rataya a wuyansu na doka da kyawawan halaye, su tsoma baki domin ceto da fararen hula a Gaza.

Ofishin watsa labarun na hukuma a Gaza ya  kuma yi kira da a tseratar da mutanen na Gaza daga yunuwar da suke fuskanta, ta hanyar yin matsin lamba da a bude hanyoyin shigar da kayan taimako da agaji cikin yankin.

Ita kuwa hukumar lafiya ta yanki ta sanar da yadda sojojin na HKI suke ci gaba da kai hare-hare akan  asibitoci da sauran cibiyoyin kiwon lafiya da hakan ya sabawa dokokin yaki.

Ofishin watsa labaru na hukumar Gaza ya kuma sanar da cewa; Har yanzu yankin yana fama da matsanancin killace shi da aka yi, da hana shigar da kayan agaji.

Daga lokacin sake komawa yaki na bayan nan da HKI ta yi, tun kwanaki 80 da su ka gabata,mutane 58 sun rasa rayukansu saboda rashin abinci mai gina jiki, sai kuma wasu 242 da yunuwa da rashin magani su ka kashe,mafi yawancinsu wadanda su ka mayanta.  Haka nan kuma wasu mata masu ciki fiye da 300 su ke cikin nasu ya zube saboda rashin abinci mai gina jiki.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Hukumar DSS Ya Kaddamar Da Cibiyar Koyar Da Addinin Musulunci A Kaduna 
  • Fiye Da Mata 300 Ne Cikinsu Ya Zube Saboda  Rashin Abinci Mai Gina Jiki A Gaza
  • Shekaru 10, Kofuna 16 Kevin De Bruyne Ya Yi Bankwana Da Manchester City
  • An Kaddamar Da Bikin Baje Kolin Aikin Gona Na Kasa Da Kasa Na Cote d’Ivoire
  • Mohamed Salah Ya Zama Gwarzon Ɗan Wasan Firimiyar Ingila Na Bana
  • Guterres: MDD Ba Za Ta Shiga Duk Wani Shiri Da Ba Zai Girmama Dokokin Kasa Da Kasa Ba A Gaza
  • Kotu ta bai wa EFCC izinin binciken sayar da filin musabaƙar Alƙur’ani na N3.5bn a Kano
  • SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (2)
  • Masanan Najeriya Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwar Afirka Da Sin A Fannin Tinkarar Kalubalen Harajin Kwastam Na Amurka