Hakar man Kolmani: Jihohin Bauchi da Gombe sun gana da NNPC kan bukatun al’umma
Published: 24th, May 2025 GMT
Jami’an gwamnati daga jihohin Gombe da Bauchi sun gudanar da wani taron kwana biyu tare da wakilan kamfanin NNPC da Kamfanin AOML, waɗanda ke gudanar da aikin hakar danyen mai a yankin Kolmani.
An kira taron ne don neman ƙarin bayani kan matakan da AOML ta riga ta ɗauka da kuma gyara kura-kuran da aka gani daidai da Dokar Masana’antar Man Fetur (PIA), da nufin kauce wasau matsalolin da suka addabi sauran yankuna masu arzikin mai.
Wata sanarwa da Kwamishinan Ma’adinai da Makamashi na Jihar Gombe, Sanusi Ahmed Pindiga, ya fitar, ta ce Kwamitin Haɗin Gwiwa da ke wakiltar jihohin biyu ya gano muhimman fannoni huɗu da ke kawo damuwa, waɗanda suka haɗa da sayen filaye, rashin gudanar da ‘Yancin Aiki (FTO), rashin bin ka’idojin Alhakin Ci Gaban Al’umma (CSR) daga AOML, da kuma gibin sadarwa.
Ya ƙara da cewa don magance matsalolin da aka gano, Kwamitin Haɗin Gwiwa ya yanke shawarar cewa za a kammala sayen filaye da zarar AOML ta samar da takardun biyan kuɗi da suka dace, yayin da NNPC zai ta bi diddigin kamfanin kan biyan kuɗin FTO don hakar mai.
Jami’an Sibil Difens sun bude wuta a garin Jos Za mu gina mayankar dabbobi ta Naira biliyan 3 a Gombe —GwamnatiA cewarsa, za a gudanar da cikakken binciken buƙatu a cikin al’ummomin masu makwabtaka da rijiyar man da waɗanda suka fuskanci matsaloli a sakamakon aikin hakar man don jagorantar shirye-shiryen ayyukan Alhakin Ci Gaban Al’umma (CSR).
Bugu da kari, za a kafa tsarin sadarwa don tabbatar da ingantacciyar mu’amala tsakanin masu gudanar da aikin Filin Mai na Kolmani da dukkan masu ruwa da tsaki.
“Mahalarta taron sun nuna godiya ga shiga tsakani a kan lokaci kuma sun sake jaddada jajircewarsu ta haɗin gwiwa don tabbatar da cewa aikin Filin Mai na Kolmani ya ci gaba ta hanyar da za ta amfani dukkan masu ruwa da tsaki kuma ta bi doka,” in ji Pindiga.
Ya ƙara da cewa: “Sun kuma sake jaddada fatansu cewa burin samun mai da iskar gas na Arewacin ƙasar da aka daɗe ana jira zai tabbata, kuma zai kawo ci gaban tattalin arziki ga yankin.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Arewa
এছাড়াও পড়ুন:
Yara miliyan 5.4 na fama da karancin abinci a jihohin arewa 9 – Red Cross
Kungiyar bayar da agaji ta kasa da kasa ta Red Cross ta ce akwai yara akalla miliyan biyar da dubu 400 da ke fama da matsalar karancin abinci a jihohi tara na arewacin Najeriya da ke fama da matsalar tsaro.
A cewar kungiyar, jihohin su ne Borno, Adamawa, Yobe, Sokoto, Katsina, Zamfara, Neja, Binuwai da kuma Kano.
Mai rikon mukamin Darktan Lafiya da Kula na kungiyar Dr Aminu Abdullahi, shi ne ya bayyana hakan a yayin taron gangamin neman tallafi kan karancin abinci na kungiyar na shiyyar Arewa maso Yamma da ya gudanar a Kano ranar Talata.
Kwanan nan gwamnati za ta sake kara kudin lantarki a Najeriya – Minista Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikaciyar ofishin jakadancin Ghana a AbujaYa ce daga cikin adadin, akalla yara miliyan daya da dubu 900 ne kuma ke fama da matsanancin karancin abincin, yana mai bayanin cewa akwai alaka mai karfi tsakanin rashin tsaro da karancin abinci.
Dr Aminu ya ce, “Munahimci cewa yaduwar cutar yunwa da sauran cututtuka kamar su maleriya da amai da gudawa da kuma kalubalen tsaro a wasu sassa na Najeriya, ya zama wajibi a dauki matakan kariya da kuma wayar da kan jama’a ta hanyar hada kai da mutane domin lalubo bakinn zaren.
“Duk inda ake da matsalar tsaro, mutane kan kyale gonakinsu su bar yankunan. Sannan mutane da dama sun rabu da muhallansu sun koma ’yan gudun hijira a wasu wuraren. To duk lokacin da aka raba ka da hanyar samun abinci, akwai barazanar fuskantar matsalar yunwa.
“Sannan ba wai iya maganar abinci kawai ake ba, magana ce ta abinci main gina jiki da kuma ruwan sha mai tsafta,” in ji shi.
Shi ma shugaban kungiyar na Najeriya, Prince Oluyemisi Adetayo Adeaga, ya ce karancin abinci babbar cuta ce da ke bukatar agajin gaggawa saboda kada ta ta’azzara.
“Idan ka je asibitocin gwamnati da na masu zaman kansu, za ka ga yadda jama’a ke tururuwar zuwa saboda cututtukan da ke da alaka da yunwa. Hakan na da barazana ga dan Adam da ci gaban kasa,” in ji shugaban.
Shi ma shugaban kungiya a Kano, Barista Salisu Sallama, ya ce kodayake jihar ba ta da yawan masu fama da cutar idan aka kwatanta da takwarorinta, amma akwai barazana idan aka yi la’akari da halin da ake ciki da zai iya ta’azzara matsalar.