An dai fara goyon bayan tazarcen Tinubu a wurin taron lokacin da mataimakin shugaban majalisar dattawa, Barau Jibrin, ya ce babu wani gurbi a fadar shugaban kasa a 2027.

Barau ya ce, “A bayyane yake a 2027, za mu sami gagarumar nasara, In Sha Allah. Don haka, mu ci gaba da hanyar da muke kai. Mu hada kai da juna, mu yi aiki tare da shugaban kasa, mu yi aiki tare da kowa, mu hada kai a tsakaninmu don samun nasarar da ake bukata.

Sanata Barau ya ci gaba da cewa sauya shekan wasu shugabannin jam’iyyun adawa zuwa APC ya kasance sakamakon aikin Shugaba Tinubu a cikin shekaru biyu kawai da ya shafe a kan karagar mulkin Nijeriya.

Kazalika, Ganduje ya ce Shugaba Tinubu na da kishin ci gaban Arewa Maso Yamma da dukkan yankin Arewa da ma Nijeriya gaba daya, don haka ya cancanci wa’adin mulki na biyu.

Ya ce yi matukar yin kokari ta hanyar wasu ayyukan da gwamnatisa ta bijiro da su, tun daga kan samar da kayayyakin more rayuwa har zuwa bunkasa bangaren noma a yankin Arewa.

Ganduje ya jaddada cewa kafa ma’aikatar bunkasa yankin Arewa Maso Yamma alama ce a fili na cewa shugaban kasa yana son yankin Arewa Maso Yamma.

Haka kuma, Gwamna Uba Sani ya ce yankin Arewaci Maso Yammaci ya bunkasa a karkashin jagorancin Shugaban kasa Tinubu.

“Shugaba Tinubu ya karbi iko ne lokacin da al’amuran kasarmu suka kasance mafi munin kalubale a tarihinta,” in ji shi.

Ya yaba da canje-canje masu amfani na Tinubu, yana cewa, “Shugaban ba ya jin tsoron yanke shawara masu wahala. ‘Yan Nijeriya ma sun fara fahimtar cewa Mai Girma Shugaba yana da kyawawan manufofi ga kasarmu.”

A nasa jawabin, shugaban majalisar wakilai, Abbas Tajudeen, ya ce ficewar wasu daga jam’iyyun adawa zuwa APC ya nuna karuwar yarda da ‘yan Nijeriya ke nuna wa jam’iyyar da shugabancinta, amma ya jaddada cewa jam’iyyar dole ne ta karfafa yawan masu goyon baya tun daga mataki na kasa.

A cikin martaninsa, shugaban jam’iyyar ADC, Dakta Ralphs Okey Nwosu, ya ce Tinubu bai cancanci yin tazarce ba.

Nwosu, a wata tattaunawa ta wayar tarho da manema labarai, ya ce idan aka duba matsayin shugaban kasa bisa kashi, yana iya samun kashi 10 kacal cikin dari sakamakon rashin tsinana abun kirki na shugabancin kasar nan.

Da yake magana kan goyon bayan shugaban kasa daga masu ruwa da tsaki na APC a Kaduna, Nwosu ya ce ‘yan adawa ne kadai za su iya ceto kasar nan, yana mai cewa idan har APC ta ci gaba da mulki a 2027, mutane da yawa daga cikin ‘yan Nijeriya za su mutu da yunwa.

Amma jam’iyyar SDP ta ce ‘yan Nijeriya za su tantance wane ne zai yi nasara a zaben shugaban kasa na 2027 idan lokaci ya yi.

Sakataren yada labarai na jam’iyyar, Araba Rufus Aiyenigba, ya shaida hakan, inda ya ce, “Mutanen Nijeriya ne za su tantance wanda zai zama shugaban kasan Nijeriya a 2027, ba shugabannin APC ba,” in ji Aiyenigba.

Sakataren yada labarai na NNPP, Ladipo Johnson, ya ce goyon baya daga cikin gida na jam’iyya na da karancin tasiri wajen gwada gwazon gwamnati.

Shi kuwa wani mamba na kwamitin zartarwa na jam’iyyar PDP, Tim Osadolor ya ce goyon bayan Shugaba Tinubu ba zai haifar da komai ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Arewa Maso Yamma yankin Arewa yan Nijeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Bidiyon tsiraici: Babiana ta sake jawo ce-ce-ku-ce

A ƙarshen makon da ya gabata ne fitacciyar ’yar TikTok wacce aka fi sani da Babiana ta fitar da wani sabon bidiyo tana rusa ihu tana kira ga Shugaba Bola Tinubu da wasu mawaƙan kudancin Najeriya da su shiga tsakaninta da ’yan Arewa a kan abin da tace suna yi mata na cin zarafi tun bayan bayyanar bidiyo tsiraicinta a shekarar 2024.

Babiana ta yi bidiyon ne cikin harshen Ingilishi inda ta ce ba a yi mata adalci a Arewa kuma ana barazana da rayuwarta.

Sojan Isra’ila ya kashe kansa saboda firgicin yaƙin Gaza Wata bas mai daukar fasinja 56 ta yi hatsari a Jos

Ta bayyana cewa tsawon shekara ɗaya ta yi tana raɓe-raɓe saboda ba ta son maganganun da mutane ke mata tun bayan bayyanar bidiyon tsiraicin nata a soshiyal midiya.

“Ina cikin halin ƙunci da damuwa, ’yan Kudu ku taimaka min Musulman Arewa na son ganin bayana” a cewar Babiana cikin harshen Ingilishi.

Yar TikTok ɗin ta ƙara bayyana cewa tun bayan ɓullar bidiyon tsiraicin nata ta shiga cikin damuwa inda kusan kullum cikin kuka take kwana, kuma har yanzu ’yan Arewa suna mata barazana da bidiyon.

Sabon bidiyo nata ya tayar ƙura, inda wasu ke ganin kalaman nata ba su kamata ba, kuma babu adalci a ciki, kuma ba ta ɗauko hanyar shawo kan matsalar ba.

Nasiru Salisu Zango, sharhi ya yi akan lamarin inda ya ce “ko da yake a cikin bidiyon Babiana ta yi maganganu na ɗora alhaki kan al’ummar Arewa Musulmai wanda hakan rashin adalci ne, amma fa duk da haka akwai buƙatar jan hankalin masu yaɗa bidiyon kan suji tsoron Allah.”

Ya ƙara da cewa “ya kamata a tausaya mata tun kafin ta faɗa wani yanayin na daban, mun sani tana da ’ya’ya da ’yan uwa da wannan yaɗa bidiyon zai iya rikita wa rayuwa.”

Shi kuwa Bilyaminu Ayuba, cewa ya yi ai dama alhaki kuikuyo ne kuma Babiana ba ta ɗauko hanyar da ya kamata ba wajen gyaran wannan matsalar duk da ya bayyana cewa abin da ake matan bai dace ba.

“ A ganina Babiana ba ta ɗauko hanyar gyara matsalar ba saboda shi mutumci madara ne, idan ya zube shi ke nan kuma har yanzu tana son shisshigi da aibanta mutane shi ya sa kullum za a dinga sukar ta da wannan bidiyon nata na marke.

“Idan har tana son zaman lafiya a rayuwarta, to dole ta daina jifa da shisshigi wa mutane, wannan shi ne. Allah Ya sa mu dace.”

Jamilu Sani a nasa ɓangaren cewa ya yi “a cikin lamarinki akwai wa’azi. A baya kece mai yaɗa bidiyon waɗansu idan sun yi irin wannan abin da kika kira kuskure, yau sai Allah Ya kama ki domin ki ji yadda kika jiyar da ’yan uwanki mata marasa tarbiyya da tunanin gobe.”

Ya ƙara da yin kira ga sauran mutane cewa Babiana da ire-irensu marasa “hangen nesa, sun yi aiki marar kyau a ɓoye. Sun yi wa kansu bidiyo, idan suka tuba , tuba na gaske, sai Allah Ya yafe musu.”

Hafsat Muhammed cewa ta yi, “Ita har ta manta duk abubuwan da ta yi wa mutane, kuma har yau ba ta nemi yafiyarsu ba har tana ma kanta kirari da ‘Queen of Update.’”

Abdulwahab Sa’id Ahmad a shafinsa na Facebook wallafawa ya yi cewa: “Wanda yake da cutar Depression ba shi yake ganewa ba sai dai a gane masa.

“Mahaukaci bai san yana hauka ba sai dai a ba shi labari bayan ya warke

“Ki bar nunawa cewa Musulmi sun yi watsi da ke da ’yan Arewa, ke ce ki ka zaɓi ki zauna a yadda ki ke.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Bidiyon tsiraici: Babiana ta sake jawo ce-ce-ku-ce
  • Ƴan Arewa Za Su Yi Murna Idan Na Zama Shugaban Ƙasa — Peter Obi
  • Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson
  • Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC
  • Al’ummar A sassan Duniya Sun Gudanar Da Zanga-Zangar Goyon Bayan Falasdinawa
  • ‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027
  • Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa
  • Tinubu ko ɗansa zai naɗa shugaban INEC, APC sai ta faɗi zaɓen 2027 — Dalung
  • ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa
  • Shirin Tinubu Kan Kiwon Dabbobi Zai Samar Da Ayyukan Yi Miliyan 5 Ga Matasa – Jega