HausaTv:
2025-05-24@21:56:12 GMT

Afrika ta Kudu ta karyata ikirarin Trump na kisan kiyashin fararen fata

Published: 24th, May 2025 GMT

Afrika ta kudu ta karyata ikirarin da shugaba Donald Trump na Amurka ya yi kan cewa kasar ta aikata kisan kiyashi kan manoma fafaren fata a Afrika ta Kudun.

Ministan ‘yan sandan Afirka ta Kudu, Senzo Mchunu, ya yi fatali da ikirarin naTrump, yana mai cewa bai da tushe balle makama, in ji jaridar Daily Maverick ta Afirka ta Kudu.

Ministan ‘yan sandan Afirka ta Kudu ya fada jiya Juma’a cewa babu wani abu da ya yi kama da hakan a game da ikirarin da Trump na kisan kiyahsin fararen fata a yayin ganawarsa da shugaban Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa. 

Trump dai ya nuna wani faifan bidiyo yayin ganawarsa da takwaransa na Afrika ta Kudu, inda har ma ya nuna hotunan wasu gawawaki a gefen titi, wadanda ya danganta da manoma farar fata da aka kashe.

Mista Mchunu ya ce karyar da Mista Trump ya yi na daga cikin “labarinsa na kisan kare dangi” – yana mai nuni da zarge-zargen mara tushe da shugaban Amurka ya yi na cewa akwai wani kamfen da ya bazu a Afirka ta Kudu na kashe fararen fata tare da kwace musu gonakinsu, wanda ya ce ya yi daidai da kisan kare dangi.

Awani labarin kuma wasu kafofin yada labarai sun ce wasu hotunan da Trump ya nuna basu da alaka da wani abu da ya faru kamar haka Afrika ta Kudu.

Kamfanin dinacin labaren Reuters ya ce wani hoton tsohon labarinsu ne na wani lamari da ya faru a RDC.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Rashin abinci mai gina jiki a Gaza ya yi sanadiyar mutuwar mutane 299

Ofishin yada labaran Gaza ya bayar da rahoton mutuwar Falastinawa 299 da suka fada cikin mawuyacin hali na rashin abinci mai gina jiki, da karancin kayan masarufi da magunguna.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya nakalto daga tashar talabijin ta Aljazeera na cewa, taimakon jin kai na cikin hadarin rubewa saboda haramcin da gwamnatin sahyoniyawan ta kakabawa na shiga Gaza a yayin da al’ummar zirin ke fama da yunwa.

Ofishin yada labarai na Gaza ya kara da cewa: Gwamnatin Sahayoniya ta yi ikirarin cewa ta ba da izinin shigar da ayarin motocin agaji yayin da manyan motoci 300 ne kawai suka shiga zirin Gaza.

Gwamnatin mamayar ta tilasta wa ayarin motocin agaji bin hanyoyin da ke da hatsarin gaske.

Har ila yau gwamnatin na kai hari kan kungiyoyin ceto, kuma a baya-bayan nan masu ceto shida sun yi shahada a bakin aikinsu, in ji rahoton.

Wannan lamarin ya haifar da mummunan sakamako, ciki har da mutuwar Falasdinawa 58 daga rashin abinci mai gina jiki da kuma wasu 242 saboda karancin magunguna da abinci.

Sojojin Isra’ila sun sake kai hare-hare a Gaza a ranar 18 ga Maris, inda suka kashe dubban Falasdinawa, tare da raunata wasu da dama, bayan da suka rusa yarjejeniyar tsagaita bude wuta na tsawon watanni 2 da kungiyar Hamas ta Falasdinu da kuma yarjejeniyar musayar fursunonin Isra’ila da Falasdinawa da aka sace.

Akalla Falasdinawa 53,822 aka kashe, akasari mata da yara, da kuma wasu mutane 122,382 da suka jikkata a mummunan harin da sojojin Isra’ila suka kai a Gaza tun ranar 7 ga Oktoba, 2023.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rashin abinci mai gina jiki a Gaza ya yi sanadiyar mutuwar mutane 299
  • Donal Trump Ya Kori Gomomi Daga Cikin Ma’aikata A Majalisar Tsaro Ta Kasar Amurka
  • Maariv: Tattaunawa A Tsakanin “Isra’ila” Da Kasashen Afirka Ta Yi Nisa Akan Hijirar Mutanen Gaza
  • A Yemen An Yi Gangamin Miliyoyin Mutane Na Nuna Goyon Bayan Falasdinawa
  • ‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027
  •  MDD Ta Nuna Damuwa Akan Tabarbarewar Yanayin “Yan Hijira A Gabashin  Kasar Chadi
  • Dangote ya sake rage farashin man fetur
  • Trump Zai Shirya Liyafar Musamman Ga Manyan Ƴan Crypto 
  • Gwamnatin Afirka Ta Kudu Ta Musanta Zargin Cin Zarafin Turawa ‘Yan Kasar Fararen Fata