Afrika ta Kudu ta karyata ikirarin Trump na kisan kiyashin fararen fata
Published: 24th, May 2025 GMT
Afrika ta kudu ta karyata ikirarin da shugaba Donald Trump na Amurka ya yi kan cewa kasar ta aikata kisan kiyashi kan manoma fafaren fata a Afrika ta Kudun.
Ministan ‘yan sandan Afirka ta Kudu, Senzo Mchunu, ya yi fatali da ikirarin naTrump, yana mai cewa bai da tushe balle makama, in ji jaridar Daily Maverick ta Afirka ta Kudu.
Ministan ‘yan sandan Afirka ta Kudu ya fada jiya Juma’a cewa babu wani abu da ya yi kama da hakan a game da ikirarin da Trump na kisan kiyahsin fararen fata a yayin ganawarsa da shugaban Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa.
Trump dai ya nuna wani faifan bidiyo yayin ganawarsa da takwaransa na Afrika ta Kudu, inda har ma ya nuna hotunan wasu gawawaki a gefen titi, wadanda ya danganta da manoma farar fata da aka kashe.
Mista Mchunu ya ce karyar da Mista Trump ya yi na daga cikin “labarinsa na kisan kare dangi” – yana mai nuni da zarge-zargen mara tushe da shugaban Amurka ya yi na cewa akwai wani kamfen da ya bazu a Afirka ta Kudu na kashe fararen fata tare da kwace musu gonakinsu, wanda ya ce ya yi daidai da kisan kare dangi.
Awani labarin kuma wasu kafofin yada labarai sun ce wasu hotunan da Trump ya nuna basu da alaka da wani abu da ya faru kamar haka Afrika ta Kudu.
Kamfanin dinacin labaren Reuters ya ce wani hoton tsohon labarinsu ne na wani lamari da ya faru a RDC.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ba Bu Dalilin Da ASUU Za Ta Fara Yajin Aiki, An Biya Duk Buƙatunsu – Ministan Ilimi
Ministan Ilimi, Dokta Tunji Alausa, ya caccaki matakin da kungiyar malaman jami’o’i (ASUU) ta dauka na fara yajin aiki na tsawon makonni biyu, yana mai bayyana matakin a matsayin wanda bai kamata ba kuma bai dace ba ganin irin kokarin da gwamnatin tarayya ke yi na biyan kusan dukkanin bukatun kungiyar. Da yake magana a wani shiri na gidan Talabijin na Channels, ‘The Morning Brief’ a ranar Litinin, Alausa ya bayyana rashin jin dadinsa da matakin da ASUU ta dauka na tsunduma yajin aiki duk da kokarin da gwamnatin ke yi akansu. “A cikin shekaru biyun da suka gabata, babu wani batun yajin aikin ASUU, saboda kokarin da gwamnati ke yi akan biyan duk bukatunsu. “A cikin sa’o’i 24 da suka gabata, ni da mataimakin shugaban kwamitin tattaunawa na gwamnatin tarayya, mun tattauna da ASUU, zan iya gaya muku a yau, a zahiri, an biya kusan dukkan bukatun ASUU, don haka ban ga dalilin da ya sa ASUU ta fara yajin aikin ba.” In ji Ministan ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano October 13, 2025
Ra'ayi Riga Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang October 13, 2025
Labarai Ba Gudu Ba Ja-da-baya Kan Ci Gaba Da Kwaskwarima Ga Tsarin Haƙar Ma’adanai – Minista October 13, 2025