Kasashen Sin da na ASEAN sun kammala tattaunawa game da kafa yankin ciniki cikin ‘yanci na Sin da ASEAN (CAFTA) karo na 3, wanda ke aikewa da sako mai karfi na goyon bayan gudanar ciniki cikin ‘yanci da hadin gwiwa mai bude kofa.

A cewar Mao Ning, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, hakika wannan labari ne mai dadi, tana cewa, wani muhimmin mataki ne na rattaba hannu kan yarjejeniyar daukaka yankin a karo na 3.

Ta kara da cewa, Sin da kasashen ASEAN, dukkansu masu goyon bayan dunkulewar tattalin arzikin duniya ne da cudanyar bangarori da dama, haka kuma yankin na CAFTA na 3, zai taimakawa Sin da kasashen wajen kara zurfafa budewa juna kofa da samun ci gaba da wadata. (Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kofin kofi mafi tsada a duniya ya shiga kasuwa a kan Naira miliyan 1.5m

Wani gidan shan kofi a birnin Dubai ya fara sayar da kofi guda na haɗaɗɗen kofi a kan kusan Dala 1,000, wato kimanin Naira miliyan 1.5, wanda da haka ya zama mafi tsada a duniya.

Gidan shan kofin mai suna Julith Café — da ke cikin unguwar masana’antu da ya zama sabuwar cibiyar masu son kofi, shi ne ya ƙaddamar da wannan sabon nau’in abin sha mai daraja.

Ana sa ran gidan shan kofi ɗin zai fara ba da wannan abin sha ga mutane kimanin 400 kacal, ciki har da wani ɗan adadi da aka tanadar wa dangin gidan sarautar Dubai.

Wani daga cikin masu mallakar gidan, Serkan Sagsoz, ya ce sun zaɓi Dubai ne saboda “birni ne da  ya dace da irin jarin da ke nuna ƙawa da kuma salo.

“Mun ga Dubai a matsayin wuri mafi dacewa don wannan kasuwanci. Wannan birni ne da ke son abubuwan da suka bambanta,” in ji Sagsoz.

’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi Amurka ta sanya Najeriya cikin ƙasashen da ake yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi

Kofin kofi ɗin, wanda ake sayarwa a kan Dirhami 3,600 (kimanin 980), an yi shi ne daga ’ya’yan kofi na musamman da ake kira Nido 7 Geisha ,daga ƙasar Panama — waɗanda aka saya a gasa ta duniya bayan tashin rububin mai tsanani tsakanin masu saye.

Kamfanin Julith Café ya ce ya biya kimanin Dirhami miliyan 2.2 (dala 600,000) don sayen kilo 20 na waɗannan ’ya’yan kofi, abin da ya kafa sabon tarihin farashi mafi tsada da aka taɓa sayen kofi a duniya.

Sagsoz ya bayyana cewa kofi ɗin yana da ƙamshi da ɗanɗano na musamman. “Yana da ƙamshin furanni farare irin na jasmine, ɗanɗanon lemo da bergamot, har da ɗanɗano irin na apricot da peach. Kamar zuma yake — laushi kuma mai daɗi sosai.”

A bara, wani gidan kofi mai suna Roasters ya kafa tarihin Guinness na kofin kofi mafi tsada a duniya a Dubai, inda ya sayar da shi a kan Dirhami 2,500, amma yanzu Julith Café ta karya wannan tarihin.

Wasu mazauna Dubai sun ce duk da abin mamaki ne, amma abin ba baƙo ba ne a garin da aka sani da abubuwan alfarma.

“Abin mamaki ne amma ai wannan Dubai ce,” in ji wata mazauniya mai suna Ines.

“Ai akwai masu kuɗi, wannan wani sabon abin alfahari ne kawai,” in ji wata mai suna Maeva.

Ana sa ran gidan shan kofi ɗin zai fara ba da wannan abin sha ga mutane kimanin 400 kacal, ciki har da wani ɗan adadi da aka tanadar wa dangin gidan sarautar Dubai.

Shin idan kuna da kudin za ku saya?

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al’ummar Kauru Sun Koka Game Da Karuwar Hare-hare Da Ke Barazana Ga Gonaki Da Rayuka
  • Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik
  • Larijani: Iran Ba Ta Tsoron Gudanar Da Tattaunawa, Amma Ta Zama Mai Amfani
  • An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya
  • Iran ta damu da halin da ake ciki a yankin El Fasher na Sudan
  • Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara
  • Kofin kofi mafi tsada a duniya ya shiga kasuwa a kan Naira miliyan 1.5m
  • Barcelona ta shiga zarwacin Victor Osimhen
  • M D Duniya Tayi Gargadi Game Da Gwajin Nukiliya Da Amurka Ta Sanar Za ta yi
  • Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan