Masu noman tabar wiwi na barazanar ƙona gidajenmu —Makiyaya
Published: 14th, February 2025 GMT
Makiyaya sun koka bisa abin da suka kira tsangwama da tsana da wasu manoman tabar wiwi ne suke nuna musu tare da yi musu barazanar ƙone gidajensu a inda suke zaune shekaru aru-aru.
Makiyaya Fulani sun yi ƙorafi ne bayan manoman tabar wuri sun kafa musu ƙahon zuƙa a inda suke zaune a yankin Oja-Badun da ke Ƙaramar Humumar Eleyele a Jihar Oyo, daura da garin Ogumaki na Jihar Ogun.
Shugaban Fulanin yankin, Alhaji Muhammadu Wakili ya shaida wa Aminiya cewa, jagoran manoman tabar wiwi a yankin ya sa wa Fulani makiyayan karan tsana, bayan da suka bai wa jami’an tsaro bayanan cewa, suna noma tabar wiwi a yankin.
Ya ce lamarin ya kai ga ’yan sanda sun kama yaran mutumin a gonar tasa, kuma tun daga lokacin shi da abokan sana’arsa suka uzzura musu.
Gwagwarmayar Ahmadu Haruna Zago, Bakaniken Jam’iyya An kama likita kan laifin yi wa ’yan bindiga magani a KatsinaWakili ya ce, “kimanin wata huɗu ke nan da muka bai wa ’yan sanda bayanin cewa, ana noma tabar wiwi a yankin da muke kiwo, kuma a wannan lokacin ’yan sandan sun yi nasarar kama mutum guda a gonar, wanda yaron mutumin ne.
“Tun daga lokacin suke nuna mana tsangwama, inda a makon jiya suka kashe mana shanu 12, baya ga barazanar da suke yi mana na cewa, sai sun tashe mu bayan sun ƙone mana gidaje.
“A ranar Asabar ɗin da ta gabata suka yo zuga, suka nufo rugarmu za su ƙona, amma da taimakon Allah, DPO na ’yan sandan yankin ya kawo mana ɗauki shi da jami’ansa, suka fatattake su, suka hana su yunƙurin nasu na ƙona mana gidaje.”
Wakili ya ƙara da cewa, mutanen sun daɗe suna yi masu barazana, inda suke goranta masu cewa, a baya sun ƙone masu gidaje shekaru huɗu da suka shuɗe, kuma babu abin da aka yi, don haka a yanzu ma za su sake domin babu abin da za a yi.
“Sun taɓa ƙone mana gidaje shekaru huɗu da suka wuce, shi ne yanzu suke yi mana izgilanci, suna barazanar za su sake kuma babu abun da za a yi, kuma daman kafin su kai ga kawo mana farmaki a ranar Asabar da ta gabata, shi wannan mutum ya je gidan radiyo, inda ya faɗi bayanan ƙarya a kanmu da ’yan sanda, cewa muna ɓata musu gona.
“Idan har da gaske mun shiga gonarsu mun lalata ai akwai hukuma, sai su nuna wa ’yan sanda, su ga ɓarnar da aka yi masu, amma babu ko alama, amma mu shanun da suka kashe mana da harbin bindiga da sara duk mun kai ƙara wajen ’yan sanda kuma muna da hotunansu, kuma ko a baya can yaran mutumin sun harbar mana yaranmu Fulani da ke kiwo a daji, inda suka harbe su da bindiga a ƙafa, sai da muka kai su asibiti, aka cire masu harsashi.
“Duk wannan tsangwamar da suke mana so suke mu bar wajen don su samu, su sake su ci gaba da noman tabar wiwi kamar yadda suka saba, domin sun sha alwashin sai sun kore mu daga wajen da muke zaune shekaru aru-aru.
“Tun lokacin mulkin Gowon, muke zaune lafiya a wannan yankin, ba mu da matsala da al’ummar yankin da shugabanninsu da ma jami’an tsaro domin tare muke aiki, muna ba su haɗin kai.
“Mutanen da muke da matsala da su kuma duk lokacin da aka sami akasi shanunmu suka yi ɓarna a gona, muna zuwa a tattauna a sasanta, mu a biya diyya, don haka masu noman tabar wiwni nan kaɗai ne ke tsangwamar mu, suna cewa sai sun kore mu za su sami damar yin noman tabar wiwi yadda suke so,” in ji shi.
Sarkin Fulanin na Oga Badun ya ƙara da cewa, bayan barazanar ƙone masu gidaje da mutanen suka yi, DPO ’yan sandan yankin ya hana su, ya gayyaci ɓangarorin zuwa taron zaman lafiya a yankin a ranar Litinin ɗin da ta gabata.
Sai dai kin lokacin Shugaban Ƙaramar Hukumar Eleyele ya buƙaci a yi taron a gidansa a ranar Litinin mai zuwa domin kawo ƙarshen matsalar.
“Mu Fulani a wannan yankin muna aiki tare da masu gari da jami’an tsaron ’yan sanda da na Amotekun don tabbatar da tsaro, kuma haɗin kan da muke bayarwa suna ba mu, mu ma,” in ji shi.
Muhammed Farouk shi ne sakataren Fulani makiyaya mazauna yankin Oja-Badun ya bayyana cewa, suna ƙoƙarin ganin an sami zaman lafiya shi ya sa suke bai wa ’yan sanda da Amoteku da sauran al’ummar gari haɗin kai, “komai tare ake yi da mu na ci-gaban gari duba da daɗewar da muka yi a nan.
”Amma yanzu kuma masu noman tabar wiwi su ne suka sako mu a gaba, don haka muna kira ga mahukunta da su zo su yi bincike, su kawo mana ɗauki,” in ji shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Tabar wiwi noman tabar wiwi
এছাড়াও পড়ুন:
Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar
Ko za ki fadawa masu karatu dan takaitaccen tarihinki?
An haife ni a a ‘Delta state’, na yi makarantar firamare da sakandare a Delta, sannan nayi aure a can. Yara na uku, Allah ya kawo rabuwa tsakani na da mijina. Babana dan ‘Nasarawa State’ ne, Mama ta kuma ‘yar Jihar Kano ce. Shekaruna Talatin da hudu, na tsinci kaina a masana’antar Kannywood ne shekara shida da suka wuce baya.
Me ya ja hankalinki har ki ka tsunduma cikin masana’antar Kannywood?
Saboda fim yana daya daga cikin abin da ya fara burge ni bayan aure na ya mutu, shi fim abu ne wanda yake kamar wa’azantarwa da kuma tunatarwa.
Ya gwagwarmayar farawar ta kasance?
Yadda gwagwarmayar ya kasace shi ne; na zo fim ne ba tare da tunanin yadda za ta kasance da ni ba, amma yanzu kam Alhamdulillah.
Ya batun iyaye lokacin da za ki sanar musu kina sha’awar fara fim, shin kin samu wani kalubale daga gare su?
Eh, a gaskiya na samu. Saboda mahaifiya ta da ‘yan’uwana sun ki yarda, sai da na samu na zaunar da su na fahimtar da su sannan.
Da wane fim ki ka fara?
‘Motsin Rai’ wanda Yahaya Sa’id ne yayi daraktin, da kuma Dadin Kowa.
Ya farkon farawar ta kasance?
Gaskiya na sha wahala kasancewar shi ne farkon dasa min ‘camera’.
Da su wa ki ka fara cin karo a farkon shigarki kannywood?
Bosho, su Dan’Auta da sauransu.
Kin yi finafinai sun kai kamar guda nawa?
Gaskiya ba zan iya kirgawa ba.
Cikin finafinan da ki ka fito wanne ne ya zamo bakandamiyyarki?
Kishiyar uwa, saboda na fito a mahaukaciya abun dai abun armashi.
Wane irin nasarori ki ka samu game da fim?
Dalilin fim na je gurare wanda ban da ta wannan hanya, ban yi tunanin zuwa ba.
Ko akwai wani kalubale da ki ka taba fuskanta cikin masana’antar?
Eh, kam ba za a rasa ba, to, amma Alhamdulillah.
Wane abu ne ya taba faruwa da ke na farinciki ko akasin haka, wanda ba za ki taba iya mantawa da shi ba a rayuwa?
Kamar mutuwar mahaifi na, ba zan taba iya mantawa ba har abada.
Ko kina da ubangida a masana’anyar Kannywood?
Eh, ina da shi.
Kafin shigarki masana’antar Kannywood wadanne jarumai ne suke burge ki, kuma me ya sa?
Ali nuhu, saboda yadda yake aikinsa kamar a gaske.
Mene ne burinki na gaba game da fim?
In zama babbar jaruma.
Bayan fim kina wata sana’ar ne?
Eh, ina ‘business’.
Misali wani daga cikin abokan aikinki ya ce yana sonki zai aure ki, shin za ki amince ki aure shi ko kuwa ba ki da ra’ayin auren dan fim?
Idan da so da kauna me zai hana.
Wasu na kokawa game da masana’antar kannywood, a takaice ya za ki yi wa masu karatu bayanin yadda masana’antar take, shin wace ce Kannywood ya cikinta yake?
Kannywood wata masana’anta ce wacce take kamar makaranta, kafin ka fara ta, dole sai ka mayar da hankali.
Wane kira za ki yi ga masu kokarin shiga kannywood?
Duk wacce za ta shigo ta dauka kamar koyan sana’a ce ya kawo ta, dole sai ta mayar da hankali tare da jajircewa.
Ko akwai wata shawara ko wani sako da ki ke da shi ga sauran abokan aikinki?
Sako na a gare su shi ne, su dinga rike gaskiya da amana, su sani mu kamar amana muke a hannunsu, su taya mu rike ta kima da mutuncin mu.
Me za ki ce da masoyanki masu kallon finafinanki?
Ina yi wa kowa fatan alkairi.
Muna godiya
Ni ma na gode.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA