Jam’iyyar APC A Najeriya Ta Tabbatar Da Tinubu A Matsayin Dan Takarar Shugaban Kasa A Jam’iyyar A Shekara Ta 2027
Published: 23rd, May 2025 GMT
Jam’iyyar ‘All Progressives Congress” (APC) mai Mulki a tarayyar Najeriya ta tabbatar da shugaban Bola Ahmed Tinubu a matsayin dan takarar Jam’iyyar a zaben shugaban kas ana shekara ta 2027 mai zuwa.
Shafin yada labarai na Afrika ya bayyana cewa a jiya Alhamis ce a taron Jam’iyyar wanda aka gudanar a Abuja, kuma wanda ya zo dai-dai da cika shekaru biyu da zagayensa na farko na shugabancin kasar Jam’iyyar ta nada shi Shugaba Bola Ahmed Tinubu dan shekara 73 a duniya a matsayin dan takararta a zaben na shekara ta 2027, don ya sami damar kamala shirinsa nag yare-gywaren tattalin arzikin kasar da y afara.
Shugaban Tinubu dai ya kara farashin man fetur a ranar da ya hau kan kujerar shugabancin kasar, ya kuma cire tallafin da gwamnati take yiwa farashin man, sannan ya kara haraji wanda duk sun hadu sun Sanya rayuwar mafi yawan mutanen kasar cikin bala’I wanda basu taba ganin irinsa .
Shirin nasa ya dadadawa manya-manyan cibiyoyin kudade a duniya wadanda ba ruwansu da rayuwar talaka a ko ina suke a duniya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu ya yi ta’aziyyar rasuwar Sarkin Gusau
Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya yi alhinin rasuwar Sarkin Gusau, Dokta Ibrahim Bello na Jihar Zamfara.
Sarkin ya rasu da safiyar Juma’a yana da shekaru 71.
An yanke wa mutum 3 hukuncin kisa kan kisan kai a Gombe HOTUNA: Yadda Kwankwaso ya karɓi ’yan APC zuwa NNPP a KanoMai bai wa Shugaban Ƙasa shawara kan harkokin watsa labarai, Bayo Onanuga ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa.
Ya ce Sarkin mutum ne da ya sadaukar da rayuwarsa don hidimta wa al’ummarsa.
Shugaba Tinubu ya ce rasuwar Sarkin babban rashi ne, ba wai kawai ga mutanen masarautarsa ba, har da ƙasa baki ɗaya.
Ya yaba da jajircewarsa, kyakkyawan shugabancin da sadaukarwarsa ga jama’a.
Shugaban ƙasa ya miƙa ta’aziyyarsa ga gwamnatin Jihar Zamfara, mutanen jihar, da kuma iyalan marigayin.
Ya roƙi Allah Ya jiƙan Sarkin, Ya kuma yafe masa kurakuransa.