Aminiya:
2025-07-10@11:13:32 GMT

An kashe matashi yayin rikici a ƙauyukan Kano

Published: 25th, May 2025 GMT

Rikici ya ɓarke tsakanin wasu matasa a ƙauyukan Faruruwa da Tarandai da ke Ƙaramar Hukumar Takai a Jihar Kano, inda aka kashe wani matashin har lahira.

Rikicin ya faru ne a ranar cin kasuwa kuma ya rikiɗe zuwa tashin hankali, inda aka ƙone rumfunan kasuwar.

Ko gwamnoni duka za su koma APC ba zai hana mu kayar da Tinubu a 2027 ba — Babachir.

Gwamnatin Gombe za ta taimaki ’yar shekara 14 da aka yi wa auren dole

Wani masani kan harkar tsaro, Zagazola Makama ne, ya bayyana hakan a shafinsa na X a ranar Lahadi.

Ya ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 7:45 na daren ranar 23 ga watan Mayu, 2025, a kasuwar Faruruwa.

A cewarsa, rikicin ya samo asali ne bayan wani matashi mai shekaru 28, Sani Yunusa daga ƙauyen Toho Diribo ya ziyarci budurwarsa a Tarandai.

Yayin da yake komawa gida, wasu matasa suka kai masa hari da sanda da adda.

Jami’an tsaro sun isa wajen cikin gaggawa don daƙile rikicin da kuma tabbatar da zaman lafiya.

Rundunar ’yan sandan jihar, ta fara bincike don gano musabbabin rikicin da kuma kama waɗanda suke da hannu a kisan matashin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ƙauyuka

এছাড়াও পড়ুন:

Dalilin da matan karkara a Kano suka fi son haihuwa a gida

‎Wata ƙungiya mai zaman kanta, Nigeria Health Watch ta ce ta gano har yanzu fiye da rabin matan da ke zaune a yankunan karkarar Jihar Kano sun fi son haihuwa a gida a maimakon zuwa asibiti.

‎Kungiyar ta alaƙanta hakan da al’adun mutanen, waɗanda ta ce an fi samun masu su a ƙauyuka da kuma yankunan karkara fiye da a birane.

‎Daraktar shirye-shirye ta ƙungiyar, Kemisola Agbaoye ce ta bayyana hakan ranar Litinin, yayin gabatar da rahoto a wani taron masu ruwa da tsaki don bayyana abubuwan da suka gano a binciken da suka gudanar a ƙananan hukumomi shida na jihar.

Cutar Diphtheria ta yi ajalin ƙananan yara 3 a Zariya Amurka za ta ɗauki nauyin ’yan tawaye domin yaƙi da ta’addanci

‎Ta ce taron zai taimaka wa gwamnati domin gano ɓangarorin da za ta fi mayar da hankali wajen magance matsalar mace-macen mata da ƙananan yara.

‎Kemisola ta ce, “Mun gano cewa akwai banbanci sosai tsakanin yankunan karkara da biranen da muka gudanar da bincikenmu.

“Alal misali, a wasu ƙananan hukumomi, mun gano cewa fiye da kaso 50 cikin 100 na mata masu juna-biyu har yanzu sun fi son haihuwa a gida, inda unguwar zoma ta gargajiya suke karɓar haihuwarsu.

‎“Hakan na faruwa ne duk da ƙoƙarin da gwamnati ke yi na ganin ta rage mace-mace yayin haihuwa a Najeriya.

“ Matsalar mutuwar mata a wajen haihuwa babbar matsala ce a Najeriya, musamman a Kano, inda muka gano fiye da rabin mata sun fi so su haihu a gida. Wannan muhimmin bincike ne ga ƙoƙarin gwamnati a wannan bangare.

‎“Bugu da kari, akwai kuma wasu dalilai da muka gano suna ƙara ta’azzara wannan matsalar kamar su rashin kyan hanyoyi da ma kuɗin zuwa asibiti ga matan, da kuma al’adun mutanen,” in ji Daraktar.

‎Ta kuma ce ƙungiyar tasu na bayar da shawarar ƙara mayar da hankali wajen wayar da kan mutane domin canza tunaninsu su rungumi haihuwa a asibiti.

‎Kemisola ta kuma ce taron wani ɓangare ne na shirin gangaminsu na ƙasa da ƙasa, wanda ke taimaka wa gwamnatin jihar Kano ta magance matsalolin da ke damun asibitocin sha-ka-tafi.

‎A nasa ɓangaren, Kwamishinan Lafiya na jihar, Dokta Abubakar Labaran Yusuf, ya ce yanzu haka jihar na kan aikin gina asibitocin sha-ka-tafi guda 260 a faɗin jihar, kuma tana shirin kammalawa tare da buɗe su nan da shekara mai zuwa.

‎Ya ce shirin wani ɓangare ne na ƙudurin gwamnatin jihar na ganin ta gina aƙalla ƙaramin asibiti a dukkan gundumomi 484 da ke jihar.

‎Kwamishinan ya kuma ce har ila yau, jihar na aikin ɗaga likafar ƙananan asibitoci 18 zuwa matsakaita a ƙoƙarinsu na ganin kowacce ƙaramar hukuma a jihar na da matsakaicin asibiti.

‎“Game da batun mata masu haihuwa a gida kuwa, matsala ce da ta wuce gina asibitoci ko samar musu da kayan aiki, magana ce ta canza tunanin mutanen.

“Yanzu haka akwai muhimmin aikin canza tunanin mutane ta hanyar amfani da masu riƙe da sarautun gargajiya da kuma kafafen yaɗa labarai wajen wayar da kan jama’a a kan illar haihuwa a gida da rashin zuwa asibiti,” in ji Kwamishinan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Manazaecin Kasar Amurka Ya Ce; Isra’ila Ta Sha Kashi A  Yakinta Da Jamhuriyar Musulunci Ta Iran
  • Sojoji Sun Kai Hari Maɓoyar Boko Haram A Borno, Sun Kashe Wasu ‘Yan Ta’adda
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 13 a ƙauyukan Neja
  • Ana zargin takalar faɗa tsakanin fadar Aminu Ado da Sanusi II
  • ‘Yan Gwagwarmayar Falasdinu Sun Halaka Sojojin Mamaya Biyar Tare Da Jikkata Wasu Goma Na Daban
  • Falasdinawa 13 Ne Suka Yi Shahada Wasu Da Dama Suka Jikkata A Hare-Haren Sojojin Mamayar Isra’ila A Gaza
  • Mata Da Matasa Dari Hudu Suka Amfana Da Tallafi A Gandun Albasa Kano
  • Dalilin da matan karkara a Kano suka fi son haihuwa a gida
  • Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan
  • China Ta Mayar Da Martani Kan Barazanar Trump Na Ƙarin Haraji Ga Kasashen BRICS