Aminiya:
2025-05-01@04:31:11 GMT

An kama likita kan laifin yi wa ’yan bindiga magani a Katsina

Published: 13th, February 2025 GMT

Jami’an tsaro sun kama wani ma’aikacin lafiya da ake zargi da yi wa wasu ’yan bindiga da suka raunata magani a Ƙaramar hukumar Safana ta Jihar Katsina.

Daga cikin majinyatan nasa har da ƙasurmin da ake nema Usman Modi Modi, wanda aka sanar da bada ladar Naira miliyan 50 don nemo shi.

Tirela ta murƙushe ɗaliba har lahira a Bauchi Kwastam ta lalata magungunan biliyan N100 a Ribas

A cikin wani bidiyo da wani mai sharhi kan harkokin tsaro Zagazola Makama ya samu, wanda ake zargin mai suna Lawan Ado, ya amsa laifin jinyar wasu ’yan bindiga da suka jikkata.

A cikin bidiyon, ya ce ’yan bindigar za su ɗauke shi su kai shi maɓoyarsu a duk lokacin da suke buƙatar magani don neman lafiya.

A cewarsa, ɗan bindigan da ya fara yi wa magani shi ne Usman Modi Modi bayan da shugaban ƙungiyar su ya samu raunuka a wata arangama da ƙungiyar ’yan banga ta Yan Kyanbara.

“Da farko an kai shi wani asibiti a Taskiya domin yi masa magani, amma bayan kwana biyu, sai suka kawo ni don in ƙara yi masa magani. An biya ni Naira 18,000 don kula da lafiyar waɗanda aka raunata,” cewar likitan da ake zargin.

Ado ya ƙara da cewa yana jinyar wasu manyan ’yan bindiga da suka haɗa da Mai Kudi wanda ya biya shi Naira 8,000 bayan an harbe shi a Kurfi.

Ya ce, haka ma ya yi wa Audu, mai taimaka wa Usman Modi Modi, wanda shi ma ya biya Naira 8,000.

Ya ƙara da cewa, “Dogo Mardi, wanda ya samu raunin harbin bindiga a yayin wani harin fashi da makami ya biya ni N11,000”.

Ya bayyana cewa ya yi tafiya zuwa wasu wurare domin jinyar ’yan fashi, ciki har da wanda aka bayyana da Karanboguwa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Karamar Hukumar Safana yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Ƴansanda Sun Kama Ƴan Daba 33 A Kano

CP Bakori ya gode wa al’ummar Kano saboda goyon bayan da suke ba su a ƙoƙarin su na yaƙar masu aikata laifuka tare da kira ga ci gaba da haɗin kai wajen kai rahoton abubuwan da suke zargi ga Ƴansanda.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwastam Ta Kama Jirage Marasa Matuka Da Sauran Kayayyaki Da Darajarsu Ta Haura Naira Biliyan 921 A Legas
  • Tsoffin ma’aikatan NECO na neman a biya su bashin haƙƙoƙinsu
  • Tinubu zai ziyarci Katsina
  • Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga , Sun Ceto Fasinjoji 6 A Taraba
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa da Mutane 12 Da Masu Sayar da Makamai 3 A Taraba Da Kaduna
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • Za a rataye wani soja saboda laifin kashe budurwarsa
  • Sojoji Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace, Sun Ƙwato Shanu 32 A Katsina
  • Ƴansanda Sun Kama Ƴan Daba 33 A Kano
  • Shekara 10 ina sayar da sassan jikin ɗan Adam — Wanda ake zargi