Aminiya:
2025-11-02@19:45:27 GMT

Ndume ya jinjina wa Tinubu kan bai wa ’yan Arewa sabbin muƙamai

Published: 25th, May 2025 GMT

Sanata Ali Ndume, mai wakiltar Borno ta Kudu a Majalisar Dattawa, ya yaba wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu, bisa bai wa ’yan Arewa mutum 12 manyan muƙamai a hukumomin gwamnati.

Ya ce wannan matakin ya gyara rashin daidaito da ake gani a naɗin muƙaman da shugaban ya yi a baya, wanda ya janyo damuwa a yankin Arewa.

Halin da fasinjoji ke ciki bayan hatsarin jirgin sama a Ilori Hakar man Kolmani: Jihohin Bauchi da Gombe sun gana da NNPC kan bukatun al’umma

A ranar Juma’a ne Shugaba Tinubu, ya sanar da sunayen wasu ’yan Arewa da aka naɗa shugabanni a hukumomi kamar su Hukumar Inshorar Noma ta Ƙasa (NAIC), Shirin Tallafa wa Masu Ƙaramin Ƙarfi na GEEP, da Hukumar Inshorar Ma’aikata (NSITF), da wasu cibiyoyin gwamnati.

Ndume ya ce waɗannan muƙamia sun nuna cewa Tinubu na ƙoƙarin gudanar da mulki cikin adalci da shigar da kowa cikin harkokin gwamnati.

A baya, Sanata Ndume ya fito fili yana sukar naɗin farko da Tinubu ya yi wanda ya ce ya nuna wariya da rashin bin tsarin kason muƙaman siyasa da kundin tsarin mulkin Najeriya ya tanada.

Amma a cikin wata sabuwar sanarwa da ya fitar a ranar Asabar, Ndume ya bayyana cewa yana ganin Shugaba Tinubu ya saurari koken jama’a kuma ya ɗauki matakin yin gyara.

Ya bayyana Tinubu a matsayin shugaba mai sauraro da karɓar gyara, wanda ke ƙoƙarin gyara kuskure idan aka nusar da shi.

Ndume ya ce babu wani shugaba da ba ya kuskure, amma abin da ke bambanta shugaba na gari shi ne yadda yake karɓar gyara cikin sauri.

A cewarsa, waɗannan sabbin naɗe-naɗen na nuna cewa yankin Arewa ba a bar shi a baya ba a harkokin mulkin ƙasar nan.

Sanata Ndume, ya ce wannan matakin zai taimaka wajen daidaita wakilci da tabbatar da cewa yankin Arewa na da muhimmanci a cikin gwamnatin Tinubu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yabo Yan Arewa

এছাড়াও পড়ুন:

Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta

Shugabannin Rundunar tsaro da Tinubu ya sallama sun hada da shugaban rundunar tsaro ta kasa Janar Christopher Musa da shugaban sojojin ruwa, Emmanuel Ikechukwu Ogalla da shugaban sojojin sama Hassan Abubakar.

Wadanda suka maye gurbin su da idanu ya koma kan hobbasar kwazon da za su nuna su ne shugaban rundunar tsaro Olufemi Oluyede, shugaban sojojin kasa Waidi Shaibu, shugaban sojojin ruwa Idi Abbas da shugaban sojojin sama S.K Aneke sai kuma shugaban rundunar leken asiri, EAP Undiendeye wanda ya ci-gaba da rike kujerar sa.

Yan Nijeriya sun jima suna kukan duk da kwarewa da gogewar jami’an sojojin Nijeriya da irin makuddan kudaden da gwamnati ke kashewa a sha’anin tsaro a kowace shekara amma matsalar kullum gaba- gaba take kara yi.

Yankuna da dama a Nijeriya musamman a Arewa- Maso- Yamma, Arewa- Maso- Gabas da Arewa ta tsakiya sun zama lahira kusa a bisa ga yadda barayin daji ke garkuwa da mutane, kone garuruwa da yi wa jama’a kisan kare dangi.

Gagarumar matsalar wadda tuni ta zama tamkar ruwan dare a tsayin shekaru ta ci dimbin rayuka da dukiyoyin al’umma ba adadi ba tare da samun gagarumar nasarar dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a cikin al’umma ba.

Masana tsaro sun bayyana ra’ayoyi mabambanta kan sauye- sauyen. Wasu na ganin cewa sabbin jini za su iya kawo canji, yayin da wasu suka yi gargadin cewa sauya shugabanni kadai ba zai wadatar ba idan ba a yi gyaran tsari ba.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi? October 31, 2025 Manyan Labarai Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda  October 30, 2025 Manyan Labarai Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC October 30, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • IAEA : Babu wata shaida da ke nuna cewa Iran na kera makaman nukiliya
  • Tinubu zai gana da Trump kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya 
  • Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini ba — Tinubu
  • Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu
  • Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
  • Zaɓen Tanzania: Shugaba Samia Suluhu Hassan ta yi tazarce
  • Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede
  • Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta
  • Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi?
  • An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara