Aminiya:
2025-07-09@17:44:52 GMT

Ndume ya jinjina wa Tinubu kan bai wa ’yan Arewa sabbin muƙamai

Published: 25th, May 2025 GMT

Sanata Ali Ndume, mai wakiltar Borno ta Kudu a Majalisar Dattawa, ya yaba wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu, bisa bai wa ’yan Arewa mutum 12 manyan muƙamai a hukumomin gwamnati.

Ya ce wannan matakin ya gyara rashin daidaito da ake gani a naɗin muƙaman da shugaban ya yi a baya, wanda ya janyo damuwa a yankin Arewa.

Halin da fasinjoji ke ciki bayan hatsarin jirgin sama a Ilori Hakar man Kolmani: Jihohin Bauchi da Gombe sun gana da NNPC kan bukatun al’umma

A ranar Juma’a ne Shugaba Tinubu, ya sanar da sunayen wasu ’yan Arewa da aka naɗa shugabanni a hukumomi kamar su Hukumar Inshorar Noma ta Ƙasa (NAIC), Shirin Tallafa wa Masu Ƙaramin Ƙarfi na GEEP, da Hukumar Inshorar Ma’aikata (NSITF), da wasu cibiyoyin gwamnati.

Ndume ya ce waɗannan muƙamia sun nuna cewa Tinubu na ƙoƙarin gudanar da mulki cikin adalci da shigar da kowa cikin harkokin gwamnati.

A baya, Sanata Ndume ya fito fili yana sukar naɗin farko da Tinubu ya yi wanda ya ce ya nuna wariya da rashin bin tsarin kason muƙaman siyasa da kundin tsarin mulkin Najeriya ya tanada.

Amma a cikin wata sabuwar sanarwa da ya fitar a ranar Asabar, Ndume ya bayyana cewa yana ganin Shugaba Tinubu ya saurari koken jama’a kuma ya ɗauki matakin yin gyara.

Ya bayyana Tinubu a matsayin shugaba mai sauraro da karɓar gyara, wanda ke ƙoƙarin gyara kuskure idan aka nusar da shi.

Ndume ya ce babu wani shugaba da ba ya kuskure, amma abin da ke bambanta shugaba na gari shi ne yadda yake karɓar gyara cikin sauri.

A cewarsa, waɗannan sabbin naɗe-naɗen na nuna cewa yankin Arewa ba a bar shi a baya ba a harkokin mulkin ƙasar nan.

Sanata Ndume, ya ce wannan matakin zai taimaka wajen daidaita wakilci da tabbatar da cewa yankin Arewa na da muhimmanci a cikin gwamnatin Tinubu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yabo Yan Arewa

এছাড়াও পড়ুন:

ADC: Tinubu Na Yunƙurin Raba Kawunan Masu Haɗaka Kafin Zaɓen 2027

ADC ta tunatar da Tinubu cewa da gwamnatin Goodluck Jonathan ba ta jure hamayya ba a baya ba, shi ma ba zai kai matsayin shugaban ƙasa ba, kuma APC ba za ta lashe zaɓe ba.

Jam’iyyar ta ce ya kamata shugaban ƙasa ya nuna cewa yana goyon bayan gaskiya da ‘yancin jam’iyyu a tsarin dimokuraɗiyya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Idan ADC na son lashe zaɓe dole ta bai wa ɗan Arewa takara — Okonkwo
  • Biza: UAE ta ƙaƙaba wa ’yan Najeriya sabbin takunkumai
  • Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba
  • Za A Horas Da Jami’an Tsaron Sakkwato, Kaduna Da Benue Sabbin Dabarun Aiki
  • Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense
  • Gwamnatin Tinubu na shirya mana zagon ƙasa — ADC
  • ADC: Tinubu Na Yunƙurin Raba Kawunan Masu Haɗaka Kafin Zaɓen 2027
  • Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista
  • Bidiyon tsiraici: Babiana ta sake jawo ce-ce-ku-ce
  • Bincike ya nuna ’yan Najeriya ba su gamsu da gwamnatin Tinubu ba