Aminiya:
2025-09-17@22:17:12 GMT

Ndume ya jinjina wa Tinubu kan bai wa ’yan Arewa sabbin muƙamai

Published: 25th, May 2025 GMT

Sanata Ali Ndume, mai wakiltar Borno ta Kudu a Majalisar Dattawa, ya yaba wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu, bisa bai wa ’yan Arewa mutum 12 manyan muƙamai a hukumomin gwamnati.

Ya ce wannan matakin ya gyara rashin daidaito da ake gani a naɗin muƙaman da shugaban ya yi a baya, wanda ya janyo damuwa a yankin Arewa.

Halin da fasinjoji ke ciki bayan hatsarin jirgin sama a Ilori Hakar man Kolmani: Jihohin Bauchi da Gombe sun gana da NNPC kan bukatun al’umma

A ranar Juma’a ne Shugaba Tinubu, ya sanar da sunayen wasu ’yan Arewa da aka naɗa shugabanni a hukumomi kamar su Hukumar Inshorar Noma ta Ƙasa (NAIC), Shirin Tallafa wa Masu Ƙaramin Ƙarfi na GEEP, da Hukumar Inshorar Ma’aikata (NSITF), da wasu cibiyoyin gwamnati.

Ndume ya ce waɗannan muƙamia sun nuna cewa Tinubu na ƙoƙarin gudanar da mulki cikin adalci da shigar da kowa cikin harkokin gwamnati.

A baya, Sanata Ndume ya fito fili yana sukar naɗin farko da Tinubu ya yi wanda ya ce ya nuna wariya da rashin bin tsarin kason muƙaman siyasa da kundin tsarin mulkin Najeriya ya tanada.

Amma a cikin wata sabuwar sanarwa da ya fitar a ranar Asabar, Ndume ya bayyana cewa yana ganin Shugaba Tinubu ya saurari koken jama’a kuma ya ɗauki matakin yin gyara.

Ya bayyana Tinubu a matsayin shugaba mai sauraro da karɓar gyara, wanda ke ƙoƙarin gyara kuskure idan aka nusar da shi.

Ndume ya ce babu wani shugaba da ba ya kuskure, amma abin da ke bambanta shugaba na gari shi ne yadda yake karɓar gyara cikin sauri.

A cewarsa, waɗannan sabbin naɗe-naɗen na nuna cewa yankin Arewa ba a bar shi a baya ba a harkokin mulkin ƙasar nan.

Sanata Ndume, ya ce wannan matakin zai taimaka wajen daidaita wakilci da tabbatar da cewa yankin Arewa na da muhimmanci a cikin gwamnatin Tinubu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yabo Yan Arewa

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima

Jigo a jam’iyyar NNPP, Buba Galadima, ya yi zargin cewa gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ba ta da niyyar gudanar da sahihi kuma ingantaccen zaɓe a 2027.

Galadima ya bayyana hakan ne ranar Talata a wata hira da aka yi da shi a shirin Prime Time na gidan talabijin na Arise TV, inda ya ce gwamnatin da jam’iyyar APC ke jagoranta ta kankane cibiyoyin gwamnati don amfaninta.

Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo

“Wannan gwamnati ba ta shirya gudanar da zaɓen adalci ba. Daga yadda suke tafiyar da al’amura, za ka gane yadda suke tarwatsa jam’iyyun siyasa. Wannan yana nuna cewa ba sa son a samu hamayya a lokacin zaɓe,” in ji shi.

Galadima ya kuma yi gargadi kan shirin nada wani da ya kira mai lam’a a matsayin sabon shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), yana mai cewa hakan na iya jefa ƙasar cikin rudani.

“Ina fatan ba gaskiya ba ne, domin idan wannan mutumin ya zama shugaban INEC, ka tabbata cewa wannan gwamnati na neman tayar da yaƙin basasa,” in ji shi.

Sai dai bai ambaci sunan mutumin ba.

Dangane da batun fara yaƙin neman zaɓe da wuri da wasu jam’iyyu ke yi, Buba Galadima ya zargi INEC da gazawa wajen aiwatar da tanade-tanaden dokokin zaɓe.

“Wannan batun fara yaƙin neman zaɓe kafin INEC ta ba da izini, gwamnatin da ke kan mulki ce ta fara shi. Wannan yana nuna cewa INEC ba za ta iya zama mai adalci a irin wannan yanayin siyasa da muke ciki ba,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
  • Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima
  • Ana zargin mace da kashe ’yar uwarta a kan N800 din barkono
  • Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani
  • Iran Ta Gabatar Da Sabbin Kayayyaki Guda 5 A Wajen Taron Kolin kere-kere .
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa
  • NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
  • Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago