Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kaddamar Da Rangadi A Karamar Hukumar Jahun
Published: 21st, February 2025 GMT
Kwamatin lura da kananan hukumomi na majalisar dokokin jihar Jigawa ya kaddamar da rangadi na yini biyu a karamar hukumar Jahun, domin tantance kwazon karamar hukumar ta fuskar gudanar da ayyukan raya kasa da sha’anin mulki da kashe kudade.
Shugaban kwamatin kuma wakilin mazabar Gwiwa, Alhaji Aminu Zakari, ya ce ziyarar na daga cikin ayyukan majalisa da suka hada da duba kasafin kudi da yin doka da kuma tantance abubuwan da gwamnati ta ke gudanarwa kamar yadda tsarin mulki ya tanadar.
Ya ce a lokacin wannan ziyara, kwamatin zai tantance kundin bayanan ayyukan raya kasa da rahoton zangon shekara da bayanan tarukan kwamatin tsaro da na gudanarwa.
Ya ce kwanitin zai kuma tantance bayanan ayyukan majalisar kansiloli da kuma alkaluman tattara kudaden shiga da takardun biyan kudade wato voucher daga watan October na 2024 kawo yanzu.
Alhaji Aminu Zakari ya kara da cewar, irin wannan ziyara tana bada damar ganawa gaba da gaba tsakanin bangaren majalisa da mahukuntan karamar hukuma da kuma kansiloli, dan musayen bayanai tare da bada shawarwari domin tabbatar da shugabanci nagari a matakin kananan hukumomi.
Tun farko a jawabinsa na maraba, Shugaban karamar hukumar Jahun, Alhaji Jamilu Muhammad Danmalam, ya lura cewa mu’amalarsa ta farko da ‘yan majalisa lokacin tantance kiyasin kasafin kudin 2024 ta ba shi damar samun Ilimi akan sha’anin milki, wanda hakan zai taimaka masa wajen jagorantar karamar hukumarsa cikin sauki.
Malam Jamilu Danmalam ya yi addu’a bisa fatan cewa ziyarar kwamatin za ta yi tasiri wajen inganta harkokin karamar hukumar da kuma al’ummar Jahun baki daya.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa Majalisar Dokoki karamar hukumar
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Tallafin Miliyoyin Naira Ga Ƴan NURTW da Mahauta a Jigawa
Gwamna Umar Namadi ya kaddamar da shirin tallafi guda biyu da suka kai fiye da naira miliyan 392, ga membobin kungiyar direbobi ta NURTW da kuma ƴan kungiyar mahauta a jihar Jigawa.
Wannan tallafi wani ɓangare ne na ƙoƙarin gwamnatinsa na inganta rayuwar masu sana’o’in da ke taka muhimmiyar rawa a rayuwar yau da kullum.
A wajen kaddamar da shirin a filin wasa na Dutse, Gwamna Namadi ya bayyana cewa shirin yana da manufa ta musamman domin tallafa wa jama’a kai tsaye. Ya ce ƙungiyoyin NURTW da mahauta suna da matuƙar tasiri, ba kawai ga membobinsu ba, har ma da al’umma gaba ɗaya, shi ya sa gwamnatinsa ta ga dacewar tallafa musu.
Gwamnan ya kara da cewa taimakon da aka bai wa waɗannan ƙungiyoyi zai kara habaka tattalin arzikin al’ummar jihar. Ya yabawa ƙungiyoyin bisa yadda suka tsaya tsayin daka wajen kare muradun membobinsu.
Ya bukaci shugabannin ƙungiyar da su tabbatar da sa ido sosai da kuma ganin cewa an bi dukkan sharuddan shirin. “Hakan zai tabbatar da cewa motocin sun yi aiki daidai da manufa, tare da bai wa shirin damar dorewa da kuma faɗaɗawa don amfanar da wasu a nan gaba’. In ji shi.
Gwamnan ya yaba da rawar da NURTW ke takawa a tattalin arzikin jihar, yana mai bayyana su a matsayin muhimmin ɓangare na samar da kayayyaki, ko a fannin noma, masana’antu ko kasuwanci. Ya ce babu wata harkar rarraba kaya da za ta yi tasiri ba tare da haɗin guiwar NURTW ba.
A cewarsa, gwamnatinsa na saka jari mai yawa a fannin gina hanyoyin mota, inda aka kammala ayyukan hanya guda 26 da aka gada, da kudin da ya kai sama da naira biliyan 100. Haka kuma, an ƙara bayar da kwangiloli don gina tituna 50 masu tsawon fiye da kilomita 850, da kudinsu ya haura naira biliyan 300.
Gwamnan ya bayyana cewa an fara amfani da hanyoyin makamashi masu tsafta, inda aka kusa kammala cibiyar sauya motoci zuwa CNG a jihar. Ya ce wannan cibiya za ta taimaka matuƙa wajen rage farashi da kuma tsaftace muhalli, tare da fa’ida kai tsaye ga ƴan NURTW.
A wani ɓangare na shirin, Gwamna Namadi ya kaddamar da tsarin lamuni na naira miliyan 113 ga ƴan kungiyar mahauta. Shirin zai taimaka wa mutane 53, inda manyan ‘yan kasuwar dabbobi 15 za su samu naira miliyan 5 kowanne, sai sauran 38 da za su samu miliyan 1 kowanne.
Ya ce ana sa ran wannan tallafi zai taimaka wajen bunkasa harkar kiwon dabbobi da samar da nama a jihar, har da kasuwannin nama gaba ɗaya.
Don tabbatar da dorewar wannan ci gaba, gwamnan ya bayyana shirin kafa sabuwar ma’aikatar ci gaban kiwo a jihar.
Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa a matakin farko na shirin, an raba motoci 36 na kasuwanci da darajarsu ta kai naira miliyan 279.3, tare da inshora, ga membobin NURTW karkashin tsarin lamuni na juyi da hukumar Youth Economic Empowerment da Employment ta jihar ke jagoranta.
Usman Muhammad Zaria