HausaTv:
2025-11-02@06:07:39 GMT

Rashin abinci mai gina jiki a Gaza ya yi sanadiyar mutuwar mutane 299

Published: 24th, May 2025 GMT

Ofishin yada labaran Gaza ya bayar da rahoton mutuwar Falastinawa 299 da suka fada cikin mawuyacin hali na rashin abinci mai gina jiki, da karancin kayan masarufi da magunguna.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya nakalto daga tashar talabijin ta Aljazeera na cewa, taimakon jin kai na cikin hadarin rubewa saboda haramcin da gwamnatin sahyoniyawan ta kakabawa na shiga Gaza a yayin da al’ummar zirin ke fama da yunwa.

Ofishin yada labarai na Gaza ya kara da cewa: Gwamnatin Sahayoniya ta yi ikirarin cewa ta ba da izinin shigar da ayarin motocin agaji yayin da manyan motoci 300 ne kawai suka shiga zirin Gaza.

Gwamnatin mamayar ta tilasta wa ayarin motocin agaji bin hanyoyin da ke da hatsarin gaske.

Har ila yau gwamnatin na kai hari kan kungiyoyin ceto, kuma a baya-bayan nan masu ceto shida sun yi shahada a bakin aikinsu, in ji rahoton.

Wannan lamarin ya haifar da mummunan sakamako, ciki har da mutuwar Falasdinawa 58 daga rashin abinci mai gina jiki da kuma wasu 242 saboda karancin magunguna da abinci.

Sojojin Isra’ila sun sake kai hare-hare a Gaza a ranar 18 ga Maris, inda suka kashe dubban Falasdinawa, tare da raunata wasu da dama, bayan da suka rusa yarjejeniyar tsagaita bude wuta na tsawon watanni 2 da kungiyar Hamas ta Falasdinu da kuma yarjejeniyar musayar fursunonin Isra’ila da Falasdinawa da aka sace.

Akalla Falasdinawa 53,822 aka kashe, akasari mata da yara, da kuma wasu mutane 122,382 da suka jikkata a mummunan harin da sojojin Isra’ila suka kai a Gaza tun ranar 7 ga Oktoba, 2023.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

“Muna kira ga hukumar da sauran hukumomi su tabbatar da adalci da daidaito a lokacin ɗaukar ma’aikata na gwamnatin tarayya,” in ji shi.

Shugaban Majalisar ya yaba wa Dala bisa kishin ƙasa da ya nuna, sannan ya umarci kwamitin majalisar da ya binciki lamarin tare da gabatar da rahoto domin ɗaukar mataki.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Bai Kamata Gwamnati Ta Ke Ciyo Bashi Bayan Cire Tallafin Man Fetur Ba – Sanusi II October 30, 2025 Manyan Labarai Atiku Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Sauya Sunayen Waɗanda Aka Yi Wa Afuwa October 30, 2025 Labarai Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU October 29, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada
  • PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu ’yan tsagin Wike
  • PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu da ke da alaƙa da Wike
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • HKI Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza Inda Take Kashe Falasdinawa
  • Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta
  • Gaza: hare-haren Isra’ila sun kashe mutane 100 Cikin Kwanaki Biyu
  • Ci Gaba Da Killace Gaza Bayan Tsagaita Bude Wuta Ya Janyo Mutuwar Mutane 1000 A Yankin
  • Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya