Rashin abinci mai gina jiki a Gaza ya yi sanadiyar mutuwar mutane 299
Published: 24th, May 2025 GMT
Ofishin yada labaran Gaza ya bayar da rahoton mutuwar Falastinawa 299 da suka fada cikin mawuyacin hali na rashin abinci mai gina jiki, da karancin kayan masarufi da magunguna.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya nakalto daga tashar talabijin ta Aljazeera na cewa, taimakon jin kai na cikin hadarin rubewa saboda haramcin da gwamnatin sahyoniyawan ta kakabawa na shiga Gaza a yayin da al’ummar zirin ke fama da yunwa.
Ofishin yada labarai na Gaza ya kara da cewa: Gwamnatin Sahayoniya ta yi ikirarin cewa ta ba da izinin shigar da ayarin motocin agaji yayin da manyan motoci 300 ne kawai suka shiga zirin Gaza.
Gwamnatin mamayar ta tilasta wa ayarin motocin agaji bin hanyoyin da ke da hatsarin gaske.
Har ila yau gwamnatin na kai hari kan kungiyoyin ceto, kuma a baya-bayan nan masu ceto shida sun yi shahada a bakin aikinsu, in ji rahoton.
Wannan lamarin ya haifar da mummunan sakamako, ciki har da mutuwar Falasdinawa 58 daga rashin abinci mai gina jiki da kuma wasu 242 saboda karancin magunguna da abinci.
Sojojin Isra’ila sun sake kai hare-hare a Gaza a ranar 18 ga Maris, inda suka kashe dubban Falasdinawa, tare da raunata wasu da dama, bayan da suka rusa yarjejeniyar tsagaita bude wuta na tsawon watanni 2 da kungiyar Hamas ta Falasdinu da kuma yarjejeniyar musayar fursunonin Isra’ila da Falasdinawa da aka sace.
Akalla Falasdinawa 53,822 aka kashe, akasari mata da yara, da kuma wasu mutane 122,382 da suka jikkata a mummunan harin da sojojin Isra’ila suka kai a Gaza tun ranar 7 ga Oktoba, 2023.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Yakin Gaza : Tarayyar Turai za ta sake nazari kan Yarjejeniyarta da Isra’ila
Bayan sabon farmakin da Isra’ila ta kai a zirin Gaza, kasashen Yamma na kokarin kara matsin lamba kan Isra’ila, wacce ta kauda kai kan kiraye kirayen da duniya ke yi na ta dakatar da yakin a Gaza.
Kungiyar ta EU, ta kara mastin lamba ta hanyar sake nazari kan yarjejeniyarta da Isra’ila ta tsawon shekaru 25 dake a tsakaninsu.
Tunda farko dama kasashen kasashen Canada-Faransa da Ingila sun sanar da yin Allah wadai da farmakin kasa na soja na sojojin Isra’ila a Gaza.
Baya ga hakan kuma Birtaniyya a ranar Talata ta sanar da kawo karshen yarjejeniyar ciniki cikin ‘yanci da Isra’ila.
Ita ma kiasar Sweden, ta yi kira da a kakaba takunkumi ga membobin gwamnatin Isra’ila.
Bayanai sun ce yanzu haka matakan da wasu kasashen yamma ke doka , ya hadassa sabani tsakanin kasashe 27 na Tarayyar Turai.