Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa da Amurka da HKI sun san cewa zasu sami nasara a kan kasar Iran da yaki da tuni  sun fadawa kasar sun kuma mamayeta.

Amma saboda wannan tsoron ne suka zabi tattaunawa da ita a kan shirinta na makamshin nukliya. Sannan Shirin makamacin nikliya ma daya ne kacal daga matsalolin da ke tsakanin Iran da HKI da kuma kasashen yamma musamman Amurka.

  Ya ce akwai matsaloli da dama, tana jirin ta kamala da gudu don ta bullo da wata. Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto ministan yana fadar haka a jiya da yamma ya kuma  kara da cewa, manufar Iran ta shiga tattaunawa da Amurka ita ce, samun ganin an daukewa kasar takunkuman tattalin arzikin da aka dora mata. Kuma ta zabi  hanyar diblomasiyya don samun hakan.

Arachi ya bayyana cewa kasashen yamma musamman Amurka sun dorawa kasar takunkuman tattalin arziki masu yawa, amma mafi  muhimmanci daga cikinsu su ne na makamashin nukliya, don Shirin makamashin nukliyar kasar ne Amurka ta dora mata takunkuman hana saida man fetur ta kuma rana bankunan kasar Iran da Swift, wato aikin da sauran bankunan a duniya. Kuma su ne suka fi cutar da tattalin arzikin kasar.  Daga karshe Aragchi ya bayyana cewa in akwai hanyar cira wadannan takunkuman Iran ba zata yi jiunkiri ba, amma kuma tana rayuwa da takunkuman tun shekar ta 2018. Amurka ta kasa cimma manufarta don wadannan takunkuman wanda kuma shine takurawa mutane su tashi su kifar da gwamnatin JMI wanda bai faru ba kuma ba zai faruba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji Da Masu Gadin Gandun Daji Zasu Murkushe Masu Aikata Laifuka A Kwara

Gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya ce an samar da isassun matakan tsaro domin kawar da wasu gungun miyagu da ke aikata munanan laifuka a jihar.

 

AbdulRazaq ya bayyana hakan ne yayin da ya bayyana wa masu ruwa da tsaki daga yankin Lafiagi na jihar Kwara ta Arewa kan dimbin kokarin gwamnatin jihar a wani taro da aka gudanar a Ilorin.

 

Gwamnan ya amince da damuwar al’ummar tare da tabbatar musu da matakin da gwamnati ke jagoranta kan lamarin.

 

Ya ce sojojin Najeriya za su ci gaba da kai hare-hare a dazuzzukan da aka gano a matsayin sansanin ‘yan ta’adda a Kwara ta Arewa da Kudu.

 

Gwamna AbdulRazaq ya ce ayyukan za su hada da sabbin jami’an tsaron dazuzzukan da aka horas da su a wuraren da aka kebe.

 

Ya kara da cewa, ayyukan za su fatattaki ‘yan ta’addan daga maboyarsu tare da dawo da kwanciyar hankali a yankunan da abin ya shafa, ya kuma kara da cewa za a yi taka-tsan-tsan don hana ’yan ta’adda yin katsalandan a wasu wurare.

 

Gwamnan ya bayyana cewa gwamnatin jihar na hada hannu da ofishin mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro domin kawar da barazanar da ake fuskanta a sassan jihar, musamman ma kauyukan da aka gano a kananan hukumomin Ifelodun, Edu da Patigi.

 

COV/ALI MUHAMMAD RABIU

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar China Ta Yi Watsi da Barazanar Trump Na Kakabawa Kasashen BRICS Karin Takunkuman Tattalin Arziki
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Yace Mutanen Kasarsa Suna Cikin Shiri Don Kare Kansu Da Karfi
  • HKI Tana Tana Son Ci Gaba Da Yaki Kuma Trump Yana Tare Da Shi
  • Amurka Ta Soke Dokar Da Ta Tabbatar Da Hai’at Tarirusham Cikin Jerin Kungiyoyin Yan Ta’adda
  • Sojoji Da Masu Gadin Gandun Daji Zasu Murkushe Masu Aikata Laifuka A Kwara
  • Kano ta sami rahoton cin zarafin yara 351 – NHRC
  • Sheikh Ibrahim Zakzaky Ya Taya JMI Murnar Nasara A Kan Mikiyanta
  • China Ta Maida Martani da Haka Kayakin Kiwon Lafiya Na Tarayyar Turai Shigowa Kasar
  • Akalla Mutane 52 Suka Rasa Rayukansu Saboda Ambaliyan Ruwan Sama A Jihar Texas Na Kasar Amurka
  • Al’ummar Iran Ba Zasu Amince Da Ci Gaba Da Zaman Tattaunawa Da Amurka Ba Saboda Fushin Da Suke Ciki Na Kai Musu Hari