Fiye Da Mata 300 Ne Cikinsu Ya Zube Saboda Rashin Abinci Mai Gina Jiki A Gaza
Published: 25th, May 2025 GMT
Ofishin watsa labaru na hukuma a Gaza ya yi kira ga kungiyoyin kasa da kasa da kuma kungiyoyin jin kai, da su yi aiki da nauyin da ya rataya a wuyansu na doka da kyawawan halaye, su tsoma baki domin ceto da fararen hula a Gaza.
Ofishin watsa labarun na hukuma a Gaza ya kuma yi kira da a tseratar da mutanen na Gaza daga yunuwar da suke fuskanta, ta hanyar yin matsin lamba da a bude hanyoyin shigar da kayan taimako da agaji cikin yankin.
Ita kuwa hukumar lafiya ta yanki ta sanar da yadda sojojin na HKI suke ci gaba da kai hare-hare akan asibitoci da sauran cibiyoyin kiwon lafiya da hakan ya sabawa dokokin yaki.
Ofishin watsa labaru na hukumar Gaza ya kuma sanar da cewa; Har yanzu yankin yana fama da matsanancin killace shi da aka yi, da hana shigar da kayan agaji.
Daga lokacin sake komawa yaki na bayan nan da HKI ta yi, tun kwanaki 80 da su ka gabata,mutane 58 sun rasa rayukansu saboda rashin abinci mai gina jiki, sai kuma wasu 242 da yunuwa da rashin magani su ka kashe,mafi yawancinsu wadanda su ka mayanta. Haka nan kuma wasu mata masu ciki fiye da 300 su ke cikin nasu ya zube saboda rashin abinci mai gina jiki.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa
Majalisar dattawa ta dakatar da Sanata Akpoti-Uduaghan a ranar 6 ga Maris, 2025, na tsawon watanni shida. Duk da cewa an kalubalanci lamarin a kotu, amma babbar kotun tarayya ba ta bayar da wani umarni na soke dakatarwar ba ko kuma tilasta sake dawo da ita bakin aiki.
A ranar 4 ga Satumba, 2025, Sanatar ta sanar da ofishin magatakarda akan aniyar ta na ci gaba da ayyukan majalisa, nan take, ofishin ya mika wasikar ga shugabannin majalisar dattawan.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp