Ofishin watsa labaru na hukuma a Gaza ya yi kira ga kungiyoyin kasa da kasa da kuma kungiyoyin jin kai, da su yi aiki da nauyin da ya rataya a wuyansu na doka da kyawawan halaye, su tsoma baki domin ceto da fararen hula a Gaza.

Ofishin watsa labarun na hukuma a Gaza ya  kuma yi kira da a tseratar da mutanen na Gaza daga yunuwar da suke fuskanta, ta hanyar yin matsin lamba da a bude hanyoyin shigar da kayan taimako da agaji cikin yankin.

Ita kuwa hukumar lafiya ta yanki ta sanar da yadda sojojin na HKI suke ci gaba da kai hare-hare akan  asibitoci da sauran cibiyoyin kiwon lafiya da hakan ya sabawa dokokin yaki.

Ofishin watsa labaru na hukumar Gaza ya kuma sanar da cewa; Har yanzu yankin yana fama da matsanancin killace shi da aka yi, da hana shigar da kayan agaji.

Daga lokacin sake komawa yaki na bayan nan da HKI ta yi, tun kwanaki 80 da su ka gabata,mutane 58 sun rasa rayukansu saboda rashin abinci mai gina jiki, sai kuma wasu 242 da yunuwa da rashin magani su ka kashe,mafi yawancinsu wadanda su ka mayanta.  Haka nan kuma wasu mata masu ciki fiye da 300 su ke cikin nasu ya zube saboda rashin abinci mai gina jiki.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

China Ta Maida Martani da Haka Kayakin Kiwon Lafiya Na Tarayyar Turai Shigowa Kasar

Kasar China ta maida martani ga takunkuman tattalin arziki na wasu kayakin kiwon lafiya wadanda tarayyar Turai da dorta maya.

Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalto majiyar kasar ta Chaina na fadar haka ta kuma kara da cewa gwargwadon takunkuman da suka dorawa kasar gwargwadon maida martanin kasar ta China.

Labarin ya kara da cewa wannan haramcin ba zai shafi kamfanonin turai da suke samar da kayakin aikin kiwo lafiya a cikin kasar China ba.

A cikin watan Yunin da ya gabata ne kungiyarn EU ta hana gwamnatocin kasashe  kungiyar sayan kayakin aikin likita fiye da dalar Amurka miliyon 5 tare da bukatar kasar china ta daina nuna bambanci a cikin ahrkokin kasuwanci da ke tsakaninsu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yara miliyan 5.4 na fama da karancin abinci a jihohin arewa 9 – Red Cross
  • Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikaciyar ofishin jakadancin Ghana a Abuja
  • Hukumar Abinci Ta Duniya ( WFP) Ta Jefa Wa Mutanane Kudancin Sudan Abinci Ta Sama
  • Sin Za Ta Yi Aiki Da MDD Don Samar Da Jagorancin Duniya Mai Cike Da Adalci Da Daidaito
  • Mata Da Matasa Dari Hudu Suka Amfana Da Tallafi A Gandun Albasa Kano
  • Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki
  • Dalilin da matan karkara a Kano suka fi son haihuwa a gida
  • Sojan Isra’ila ya kashe kansa saboda firgicin yaƙin Gaza
  • Falasdinawa Kimani 635 Amurka da HKI Suka Kashe A Cibiyoyin Karban Abinci A Gaza
  • China Ta Maida Martani da Haka Kayakin Kiwon Lafiya Na Tarayyar Turai Shigowa Kasar