Aminiya:
2025-04-30@23:42:28 GMT

Tirela ta murƙushe ɗaliba har lahira a Bauchi

Published: 13th, February 2025 GMT

Wata ɗalibar a Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Tarayya da ke Bauchi, Faith Aluko Adesola, ta rasa ranta bayan da wata babbar mota ta murƙushe ta.

Jami’in hulɗa da jama’a na makarantar, Alhaji Rabi’u Muhammad ne, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Majalisun Tarayya sun amince da kasafin kuɗin N54.9trn na 2025 Kwastam ta lalata magungunan biliyan N100 a Ribas

Ya ce Adesola ɗaliba ce da ke ajin farko (ND1) a Sashen Koyon Aikin Jarida na makarantar.

A cewarsa, tana kan ɗan acaba domin zuwa makaranta lokacin da babbar motar ta yi awon gaba da babur ɗin a kusa da kofar shiga makarantar, lamarin da ya yi sanadiyyar rasuwarta.

“Da muka samu labarin, tawagar makaranta da suka haɗa da shugaban tsaro da shugaban kula da harkokin ɗalibai sun garzaya wajen, amma likitan makaranta ya tabbatar da rasuwarta,” in ji Muhammad.

Direban babur ɗin ya tsira da ransa a hatsarin.

Makarantar ta sanar da iyayenta, kuma wakilanta sun halarci jana’izarta a ranar Alhamis.

Muhammad, ya ja hankalin ɗalibai da su kasance masu taka-tsantsan yayin ƙetare hanya domin gujewa irin wannan hatsari.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗalibai hatsarin mota kwaleji rasuwa

এছাড়াও পড়ুন:

ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno

Ƙungiyar ISWAP mai yaƙi da tayar da ƙayar baya a yammacin Afirka, ta ɗauki alhakin harin da ya yi ajalin mutum 26 a Jihar Borno.

Ƙungiyar ta iƙirarin ɗaukar alhakin harin ne a wani saƙo da ta wallafa a shafin Telegram kamar yadda BBC ya ruwaito.

Aminiya ta ruwaito yadda wani abin fashewa da ake zargin bam ne ya kashe aƙalla mutum 26, ciki har da mata da yara a kan hanyar Rann zuwa Gamboru Ngala da ke Jihar Borno.

Lamarin ya faru ne da yammacin ranar Litinin a lokacin da motoci suka tayar da bama-baman da aka ɗana a gefen hanyar, da ya rutsa da maza 16 da mata huɗu da ƙananan yara guda shida.

Ta yi wa saurayinta ƙaryar shekarunta 27 maimakon 47 An dawo da wutar lantarki a Sifaniya da Portugal

Majiyoyi, ciki har da wani babba soja, sun tabbatar wa kamfanin dillancin labarai na Anadolu da harin na baya bayan da safiyar ranar Talata.

Sun bayyana cewa waɗanda lamarin ya rutsa da su suna kan hanyarsu ta tafiya Gamboru Ngala ne daga Rann lokacin da suka isa inda ‘yan ta’addan ISWAP suka ɗana bam ɗin.

Bayanai sun ce baya ga mutum 26 da suka mutu, ƙarin mutum uku sun ji munanan raunuka.

“Mun tura wasu masu ba da agajin gaggawa inda lamarin ya auku domin kwashe mutane tare da tabbatar da tsaron sauran fararen-hula a wurin,” kamar yadda wata majiyar sojin da ba ta yarda a bayyana sunanta ba ta shaida wa Anadolu.

Ali Abass, wani ganau wanda ke tafiya a kan hanyar a lokacin da lamarin ya auku, ya ce sojojin da ‘yan sa-kai sun kai waɗanda suka jikkata wani asibiti.

Ya ƙara da cewa ɗaya daga cikin ‘yan’uwansa na cikin waɗanda lamarin ya rutsa da su.

Harin yana zuwa ne yayin da hare-hare ke ƙara ƙaruwa a yankin Tafkin Chadi, inda ‘yan ta’addan Boko Haram da ISWAP ke ƙara ƙaddamar da hare-haren bama-bamai da kwanton-ɓauna kan motocin fararen-hula da na sojoji.

An ba da rahoton hare-hare irin wannan a ranakun 21 ga watan Maris da 12 ga watan Afrilu. Kawo safiyar ranar Talata dai, jami’an tsaro a Borno ba su fitar da wata sanarwa a hukumance game da lamarin ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Tarayya ta ayyana hutu gobe Alhamis
  • Rashin tsaro: Gwamnan AbdulRahman Ya Gana Da Sarakuna Masu Daraja Ta Daya A Jihar Kwara 
  • ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno
  • Sojoji Sun Harbe Mutane Biyu Har Lahira Da Ake Zargi Ɓarayin Mota Ne A Filato 
  • Gwamnatin Yobe Na Ƙoƙarin Inganta Tsaro – Hon. Idi Gubana
  • ‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Mutum 8 Da Bam A Borno
  • Makafi 37 Sun Zana Jarabawar JAMB A Bauchi
  • Gwamnatin Tarayya Ta Umurci WAEC, NECO Su Koma Amfani Da CBT Nan Da 2026
  • Al-Shara Ya Ki Abincikewa Da Tsarin Tarayya Wanda Kurdawan Kasar Siriya  Suke Bukata
  • Uganda Ta Sanar Da Kawo Karshen Ebola Da Ta Barke A Kasar