Gwamnan Kano Ya Ceto Dalibai 84 Da Ganduje Yaki Biya Wa Kudin Makaranta A Cyprus
Published: 23rd, May 2025 GMT
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp.এছাড়াও পড়ুন:
An ceto matar da aka yi garkuwa da ita, da kama mutum 2 a Yobe
Rundunar ’yan sandan Jihar Yobe ta sanar da samun nasarar kuɓutar da wata mace mai shekara 22 da aka yi garkuwa da ita tare da kama wasu mutum biyu.
An kama mutum biyun ne da ake zargi da alaƙa da wani mummunan hari a ƙauyen Tashan Randa da ke ƙaramar hukumar Fika.
A cikin wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, SP Dungus Abdulkarim ya fitar, ya ce samamen da aka gudanar tare da haɗin gwiwar mafarautan yankin, ya nuna wani gagarumin ci gaba a ƙoƙarin da rundunar take yi na yaƙi da rashin tsaro a jihar.
An kama wani matashi da ya yi shigar mata a Adamawa Dangote ya sake rage farashin man feturSanarwar ta ce, a ranar 6 ga Mayu, 2025 da misalin ƙarfe 5:58 na yamma, wasu ’yan bindiga ɗauke da makamai sun kai farmaki gidan Maikudi da ke ƙauyen Tashan Randa, inda suka yi awon gaba da ’yarsa tare da raunata wata yarinya maƙwabciyarta da harbin bindiga.
Sanarwar ta ƙara da cewa, jami’an rundunar sun gaggauta gudanar da bincike, inda suka yi amfani da buƙatar kuɗin fansa da ake nema ₦5,000,000 domin gano masu garkuwa da mutanen.
“An kama wasu mutane biyu, Waiti Bello mai shekara 30 daga ƙauyen Jangalawaje da Idrissa Adamu mai shekara 35 na ƙauyen Biriri, ƙaramar hukumar Gujba, dukkansu sun amsa laifin da ake zarginsu da aikatawa, kuma suna taimakawa wajen gudanar da bincike.
“An samu nasarar gano bindigar toka guda ɗaya da babur da aka yi amfani da su wajen kai harin.
Kwamishinan ’yan sandan Jihar Yobe, CP Emmanuel Ado, ya tabbatar da ƙudurin rundunar na kawar da munanan laifuka.” Muna ci gaba da jajircewa wajen kare al’ummarmu.
Wannan nasarar ta nuna muhimmancin haɗin gwiwa tsakanin jami’an tsaro da ’yan ƙasa,” inji shi, inda ya buƙaci mazauna yankin da su bayar da rahoton abubuwan da ake zargi ga rundunar don magance lamurra kafin su kasance. Cewar CP Emmanuel.