Allah Ya Isa: Shugaban PDP Damagun ya musanta zargin yi wa APC aiki
Published: 23rd, May 2025 GMT
Shugaban babbar jam’iyyar adawa ta PDP, Umar Iliya Damagun, ya yi Allah Ya isa ga masu zargin da yi wa jam’iyya mai mulki, APC, aiki.
Wasu masu ruwa da tsaki a PDP na zargin cewa Damagun da yi wa jam’iyyar zagon ƙasa APC, shi ya sa yake rura wutar rikicin cikin gida da ya ƙi ci ya ƙi cinyewa a PDP.
Amma a yayin wata hira da ya yi da BBC, Damagun ya yi fatali da zargin, yana mai cewa Allah Zai saka masa tsakaninsa da masu yi masa wannan ƙazafi.
“Allah Ya isa tsakanina da duk wanda ya yi min wannan ƙazafi, kuma Allah Zai yi mana shari’a,” in ji shugaban na PDP, wanda ake zargi da zama ɗan-amshin-shatan APC.
Ya ce, “Da zan shiga Jam’iyyar APC, da tun lokacin Buhari na shiga,” in ji shugaban na PDP, wanda ake zargi da zama ɗan-amshin-shatan APC.
“Tun da na shiga jam’iyyar PDP a 1999 ban taɓa sauya sheƙa ba. Dole wanda ba ya so na zai nemi yadda zai yaɓa min zargi don ya samu biyan buƙatarsa. Na ce ma na je na yi mitin da Tinubu, a Ingila, wannan duk masu yin wannan na bar su da Allah,” in ji shi.
Dangantaka da Wike da sauya sheƙar mambobiDangane da zargin sa da kusanci da kuma alaƙa da Ministan Abuja kuma tsohon Gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike, da kuma yi wa PDP zagon-ƙasa, Damagun ya mayar da martani da cewa: “Duk masu zargin yau ina alaƙa da Ministan Abuja, kan na san shi ko na yi alaƙa da shi, da yawansu sun yi alaƙa da shi. Ni dai laifina guda ɗaya a nan shi ne ban yardar musu yadda suke so su yi da shi ba.”
Game da yadda wasu manyan jaga-jigan jam’iyyar suka koma jam’iyyar APC, Damagun ya ce sauya sheƙar ta ba wa jam’iyyar PDP takaici, duk da cewa babu laifin da aka yi wa masu ficewan.
Ya ce amma duk da haka jam’iyyar tana ƙoƙarin dinke ɓarakar da ta kunno kai a cikinta.
“Yawanci al’amari yana tasowa idan mutum abubuwa suka faru zai nemi dalili da zai ce shi ya tafi,” kamar yadda ya bayyana
“Babu wanda zai ce PDP ta masa laifi”Damagun ya bugi ƙirji da cewa duk waɗanda suka sauya sheƙa, babu wanda zai iya fitowa ya ce jam’iyyar ta yi masa wani laifi: “Sai dai ma ta yi musu riga ta yi musu wando.”
Ya jaddada cewa PDP ba ta da wata matsala da har ta kai a yi ɓangarori a cikinta.
Amma ya tabbatar da cewa suna da matsalolin cikin gida, domin jam’iyya ba ta taɓa rasa matsala, saboda shugabannin da mambobinta duk mutane, kuma kowa yana da buƙatunsa.
Don haka dole a samu saɓani, a kuma samu son kai, ta yadda wani idan ba a yi masa yadda yake so ba, “to kai ba ka iya ba,” in ji shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: zargi
এছাড়াও পড়ুন:
Ba mu tilasta wa kowa ya koma APC ba – Tinubu
Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya caccaki masu cewa gwamnatinsa na ingiza ’yan Najeriya wajen bin tsarin jam’iyya ɗaya, yana mai cewa ba za ka iya zargi mutane kan zaɓar jam’iyya ba.
Da yake jawabi a wajen taron ƙoli na jam’iyyar APC karo na farko da aka yi a ranar Alhamis, da ya gudana a fadar shugaban ƙasa a Abuja, shugaban ya ce “jam’iyya ɗaya ce ke mulki”.
Jami’an tsaron Zulum sun buɗe wa Boko Haram wuta a Maiduguri An ceto matar da aka yi garkuwa da ita, da kama mutum 2 a Yobe“Ga waɗanda har yanzu suke tunanin fita daga jam’iyyarsu, ƙasar nan taku ce, ku riƙe ta, ga masu maganar tsarin jam’iyya ɗaya, jam’iyya ɗaya ce ke mulkin Najeriya, ba za ku zargi mutanen da ke shirin ficewa a jam’iyyar ba.
“Na yi farin ciki da abin da muke da shi kuma ina tsammanin ƙari. Haka lamarin yake. Muna cikin tsarin mulkin demokraɗiyya.”
Ya ce, babu wanda zai iya tilasta wa kowa ya tsaya a inda bai so, ya ƙara da cewa APC a shirye take ta karɓi ƙarin ’yan Najeriya da ke son shiga jam’iyya mai mulki.
Ya ce, “Suna ganin jam’iyyar siyasa ta gaza, amma da jajircewarku, ba mu yi ƙasa a gwiwa ba, mu ne masu ci gaba, za mu yi sojan gona, ku ci gaba da yin aiki tuƙuru… Ina saurarenku ba su ba.
“Muna da damar da za mu sa Afirka ta kasance mai mai ci gaba, amma ina roƙonku da a ci gaba da tafiya tare. Ga waɗanda ba zan iya ba ma muƙaman siyasa ba, ku yi haƙuri, za ku yi farin cikin shiga wannan jam’iyya.”