Aminiya:
2025-09-18@02:16:09 GMT

Allah Ya Isa: Shugaban PDP Damagun ya musanta zargin yi wa APC aiki

Published: 23rd, May 2025 GMT

Shugaban babbar jam’iyyar adawa ta PDP, Umar Iliya Damagun, ya yi Allah Ya isa ga masu zargin da yi wa jam’iyya mai mulki, APC, aiki.

Wasu masu ruwa da tsaki a PDP na zargin cewa Damagun da  yi wa jam’iyyar zagon ƙasa APC, shi ya sa yake rura wutar rikicin cikin gida da ya ƙi ci ya ƙi cinyewa a PDP.

Amma a yayin wata hira da ya yi da BBC, Damagun ya yi fatali da zargin, yana mai cewa Allah Zai saka masa tsakaninsa da masu yi masa wannan ƙazafi.

“Allah Ya isa tsakanina da duk wanda ya yi min wannan ƙazafi, kuma Allah Zai yi mana shari’a,” in ji shugaban na PDP, wanda ake zargi da zama ɗan-amshin-shatan APC.

Ya ce, “Da zan shiga Jam’iyyar APC, da tun lokacin Buhari na shiga,” in ji shugaban na PDP, wanda ake zargi da zama ɗan-amshin-shatan APC.

“Tun da na shiga jam’iyyar PDP a 1999 ban taɓa sauya sheƙa ba. Dole wanda ba ya so na zai nemi yadda zai yaɓa min zargi don ya samu biyan buƙatarsa. Na ce ma na je na yi mitin da Tinubu, a Ingila, wannan duk masu yin wannan na bar su da Allah,” in ji shi.

Dangantaka da Wike da sauya sheƙar mambobi

Dangane da zargin sa da kusanci da kuma alaƙa da Ministan Abuja kuma tsohon Gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike, da kuma yi wa PDP zagon-ƙasa, Damagun ya mayar da martani da cewa: “Duk masu zargin yau ina alaƙa da Ministan Abuja, kan na san shi ko na yi alaƙa da shi, da yawansu sun yi alaƙa da shi. Ni dai laifina guda ɗaya a nan shi ne ban yardar musu yadda suke so su yi da shi ba.”

Game da yadda wasu manyan jaga-jigan jam’iyyar suka koma jam’iyyar APC, Damagun ya ce sauya sheƙar ta ba wa jam’iyyar PDP takaici, duk da cewa babu laifin da aka yi wa masu ficewan.

Ya ce amma duk da haka jam’iyyar tana ƙoƙarin dinke ɓarakar da ta kunno kai a cikinta.

“Yawanci al’amari yana tasowa idan mutum abubuwa suka faru zai nemi dalili da zai ce shi ya tafi,” kamar yadda ya bayyana

“Babu wanda zai ce PDP ta masa laifi”

Damagun ya bugi ƙirji da cewa duk waɗanda suka sauya sheƙa, babu wanda zai iya fitowa ya ce jam’iyyar ta yi masa wani laifi: “Sai dai ma ta yi musu riga ta yi musu wando.”

Ya jaddada cewa PDP ba ta da wata matsala da har ta kai a yi ɓangarori a cikinta.

Amma ya tabbatar da cewa suna da matsalolin cikin gida, domin jam’iyya ba ta taɓa rasa matsala, saboda shugabannin da mambobinta duk mutane, kuma kowa yana da buƙatunsa.

Don haka dole a samu saɓani, a kuma samu son kai, ta yadda wani idan ba a yi masa yadda yake so ba, “to kai ba ka iya ba,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: zargi

এছাড়াও পড়ুন:

Peter Obi ya kai wa Obasanjo ziyara

Ɗan takarar jam’iyyar Labour a zaɓen shugaban ƙasa na 2023, Peter Obi, ya ziyarci tsohon shugaban ƙasa, Olusegun Obasanjo, da kuma sabon Olubadan na Ibadan, Rashidi Ladoja, a wani zagayen ganawa da manyan ’yan siyasa gabanin zaɓen 2027.

Obi, wanda ke ƙoƙarin ƙara yauƙaƙa zumunci da manyan shugabanni a fadin ƙasar, ya bayyana cewa ziyarar na da alaƙa da burinsa na ganin an samu shugabanci na gaskiya da riƙon amana a Najeriya.

An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta

A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X, Obi ya bayyana cewa ziyararsa ta musamman zuwa Ibadan na da nufin girmama Rashidi Ladoja, wanda aka naɗa a matsayin Olubadan, da kuma jaddada muhimmancin Ibadan a siyasa, zamantakewa, da tattalin arzikin ƙasar.

“Na kai ziyara don girmama sabon Olubadan, Rashidi Ladoja, wanda ƙwarewarsa a matsayin tsohon sanata, gwamna, kuma attajiri za ta taimaka wajen ɗaga martabar Ibadan,” in ji Obi.

Ya ƙara da cewa tattaunawarsa da Obasanjo da Ladoja na da nasaba da ci gaban Najeriya da kuma shugabanci da ke da burin sauya al’umma ta fuskar gaskiya da adalci.

Ziyarar Obi na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da shirye-shiryen siyasa gabanin babban zaɓen shekarar 2027, inda ake hasashen zai sake tsayawa takarar shugaban ƙasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • UNICEF Ya Ba Da Tallafin Kayayyakin Aiki Ga Cibiyoyin Lafiya A Kirikasamma
  • Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare
  • Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
  • Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu
  • Ana zargin mace da kashe ’yar uwarta a kan N800 din barkono
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar
  • Peter Obi ya kai wa Obasanjo ziyara
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar