George Iniobong ɗan shekara ashirin da biyu daga tawagar Jihar Binuwai ya samu kyautar azurfa a gasar maza ta Judo mai nauyin kilo 60 a yau Lahadi, yayinda ake cigaba da gasar wasanni ta ƙasa karo na 22 (NSF) da ke gudana a Abeokuta, babban birnin jihar Ogun.

Nasarar da George ya samu ya sa tawagar ta Jihar Binuwai ta samu kyautukan tagulla da Azurfa 9 jimilla a gasar, wakilinmu ya ruwaito cewa, Iniobong, ya yi matuƙar taka rawar gani a wasan inda ya samu nasara a kan abokin karawarshi daga jihar Ogun cikin mintunan ƙarshe na karawar.

An Gano Kofin Gasar Zakarun Turai Na Mata Bayan Sace Shi Da Aka Yi CHINADA Ta Nuna Matukar Adawa Da Gasar Wasannin Da Aka Amince Da Kwayoyin Kara Kuzari

George Iniobong yayinda yake zantawa da manema labarai bayan samun wannan gagarumar nasarar, ya yaba wa Gwamnan Jihar Binuwai, Fr. Hyacinth Alia domin abinda ya kira gudunmawar da gwamnan ya ba shi da sauran ‘yan wasa daga jihar domin su nuna bajintarsu a wasannin na Gateway wanda ya haɗa ‘yan wasa daga dukkan jihohin kasar nan 36 da kuma babban birnin tarayya Abuja, domin fafatawa a wasanni daban-daban, da niyyar inganta hadin kai da kwazo a fadin Najeriya.

“Duk da cewar nayi tunanin samun kyautar zinare a wannan wasan amma ina sa ran kasancewa cikin masu samun wannan kyautar zuwa gaba, Nasara ta na tare dani da kuma jihar Binuwai” inji shi, “Duk da haka na ƙara samun ƙwarin gwuiwa da gogewa, kuma a shirye nake in bayar da duk abin da zan yi wajen samun nasarar jihar idan wata dama ta samu ya kara da cewa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Jihar Binuwai jihar Binuwai

এছাড়াও পড়ুন:

An ƙaddamar da tsarin inshorar lafiya na mutum 38,000 a Yobe

Gwamna Mai Mala Buni, ya ƙaddamar da tsarin inshorar lafiya na mutane 48,000 domin jaddada ƙudirin gwamnatinsa na ƙara ƙarfafa matakan kiwon lafiya a matakin farko a fadin Jihar Yobe.

Buni ya bayyana shirin fara samar da daidaito a bangaren kiwon lafiya wanda zai samar da inshorar lafiya ga mata masu rauni da yara ‘yan kasa da shekaru biyar sama da 38,000 a fadin jihar.

Dalilin da matan karkara a Kano suka fi son haihuwa a gida Cutar Diphtheria ta yi ajalin ƙananan yara 3 a Zariya

Gwamnan ya bayyana cewa an samu gagarumin ci gaba yayin da ya kaddamar da wasu sabbin tsare-tsare da nufin fadada harkokin kiwon lafiya, musamman ga marasa galihu.

Ya bayyana hakan ne a ranar Litinin yayin jawabinsa a wajen babban taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a Damaturu, wanda ya samu halartar sarakunan gargajiya da malaman addini, abokan hulda, ma’aikatan lafiya da manyan jami’an hukumar gudanarwa a bangaren samar da kiwon lafiya a matakin farko da kuma kungiyoyin farar hula.

Gwamna Buni ya bayyana manufarsa ta samar da lafiya mai rahusa a matsayin ginshikin ci gaban zamantakewa da tattalin arzikin al’umma.

Ya amince da goyon bayan gwamnatin tarayya da abokan hulda da suka hada da Gidauniyar Bill and Melinda Gates, Aliko Dangote Foundation, UNICEF, da WHO da dai sauransu.

Gwamnan ya jaddada kudirin jihar na samar da kiwon lafiya, inda ya ba da misali da kafa cibiyoyin kiwon lafiya a matakin farko guda 142, samar da kayan aiki da magunguna, da daukar kwararrun ma’aikatan kiwon lafiya sama da 2,000 a fadin Jihar.

Ya bayyana irin nasarorin da jihar ta samu ciki har da fitowar ta a matsayin zakara ta shekarar 2024 a bangaren samar da kiwon lafiya a matakin farko a fadin kasar nan ta Champion leadership for Primary Health Care PHC  2024.

Ya kuma yi tsokaci kan kafa Hukumar Kula da Inshorar Lafiya ta Jihar Yobe (YSCHMA) da Hukumar Kula da Magunguna ta Jihar Yobe (YODMA) don magance kuɗaɗen kula da lafiya da samar da magunguna.

Kazalika, ya bukaci sarakunan gargajiya da su ba da goyon baya tare da bayar da gudunmawa wajen karfafa ayyukan kiwon lafiya a matakin farko a yankunansu.

Gwamnan ya bukaci masu ruwa da tsaki da su lura da batutuwan da aka tattauna a taron tare da magance kura-kuran da ake da su a yankunansu da kuma wuraren gudanar da ayyukansu domin kara inganta harkar kiwon lafiya a matakin farko a Jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Na Biya Bashin Garatutin Naira Biliyan 13.6 Da ’Yan Fanshon Zamfara Ke Bi Tun 2011 – Gwamna Lawal
  • Har Yanzu Ba A Ga Mutum 160 Bayan Ambaliyar Texas
  • Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense
  • DAGA LARABA: Shin Ko Zafin Nema Na Kawo Samu?
  • An ceto mutum 6 daga hannun masu garkuwa a Kebbi
  • ‘ADC za ta mayar da APC jam’iyyar adawa a 2027’
  • An ƙaddamar da tsarin inshorar lafiya na mutum 38,000 a Yobe
  • Dalilin da matan karkara a Kano suka fi son haihuwa a gida
  • Cutar Diphtheria ta yi ajalin ƙananan yara 3 a Zariya
  • Kano ta sami rahoton cin zarafin yara 351 – NHRC