HausaTv:
2025-05-25@16:52:08 GMT

Ukraine Da Rasha Sun Yi Musayar Fursinoni Tsakaninsu Irinsa A Karon Farko

Published: 25th, May 2025 GMT

A jiya Asabar ce kasashen Rasha da Ukraine suka yi musayar Fursinoni a tsakanin, karon farko irinsa tun bayan fara yaki a tsakaninsu fiye da shekaru 3 da suka gabata.

Shafin yanar gizo na Labarai Arabs News ya bayyana cewa an yi musayar furisnonin ne a jiya Asabar kuma ko wace kasa ta sake fursinonin yaki har 390.

Labarin ya kara da cewa a dai dai lokacinda aka yi musayar fursinonin sojojin Rasha sun yi loguden wuta a kan birnin Kiyev babban birnin kasar ta Ukraine.

Majiyar gwamnatin kasar Ukraine ta bada sanarwan cewa akalla mutane 10 sun ji rauni saboda luguden watan.

A makon da ya gabata ne kasashen biyu suka tattauna a tsakaninsu a birnin Istambul na kasar Turkiyya, inda ake saran zasu tsagaita budewa juna wuta amma hakan bai faru ba saboda sabanin da ke tsakanin kasashen biyu. Amma duk da haka sun amince su yi musayar fursinoni a tsakaninsu wanda ya tabbata a jiya.  Ana saran kasashen biyu zasu sake haduwa nan kusa a kokarin tsagaita wuta a tsakaninsu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Bukaci Kada Amurka Ta Siyasantar Da Hadin Gwiwar Bangaren Ilimi

Ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ta ce, hadin gwiwa a bangaren ilimi tsakanin Sin da Amurka na moriyar juna ne, kuma Sin ta kasance mai adawa da siyasantar da hadin gwiwar bangaren ilimi.

Kakakin ma’aikatar Mao Ning ce ta bayyana haka yayin taron manema labarai na yau Juma’a, lokacin da aka nemi jin ta-bakinta kan matakin gwmnatin Trump na hana jami’ar Harvard daukar dalibai daga kasashen waje.

A cewar Mao Ning, ire iren wadannan matakai da Amurka ke dauka za su lalata kima da darajar kasar, tana cewa, Sin za ta nace wajen kare hakkoki da muradun dalibai da malaman kasar dake kasashen waje.

Ta kuma jaddada adawar Sin ga bata sunanta da takalarta ba gaira ba dalili, tana mai kira ga Amurka ta dage takunkumanta da suka sabawa doka. (Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Masu Zanga-Zanga A Mafi Yawan Kasashen Turai Sun Bukaci Kasashen A Kawo Karshen Kissan Kiyashi A Gaza
  • Karon farko an tattauna kai tsaye tsakanin ECOWAS da AES
  • Iran Ta Ce Warware Rikicin Falasdinu Ta Kafa Kasashe Biyu Ba Hanyace Da Ta Dace Magance Matsalar Ba
  • Maariv: Tattaunawa A Tsakanin “Isra’ila” Da Kasashen Afirka Ta Yi Nisa Akan Hijirar Mutanen Gaza
  • Sin Ta Bukaci Kada Amurka Ta Siyasantar Da Hadin Gwiwar Bangaren Ilimi
  • Kamfanoni Masu Jarin Waje Sun Ci Gajiyar Tsarin Kasar Sin Na Samar Da Rangwamen Gwamnati Ta Musayar Sabbin Kayayyaki Da Tsofaffi
  • Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Gwamnatin Jamus Friedrich Merz
  • Yan Majalisar Tarayya Na Katsina Sun Mara Wa Gwamna Dikko Radda Baya Don Takarar Zango Na Biyu
  • Sojojin Yemen Sun Kai Wa Filin Jirgin Saman “Ben Gorion” Hari Sau Biyu A Yau Alhamis