Iran Ta Ce Warware Rikicin Falasdinu Ta Kafa Kasashe Biyu Ba Hanyace Da Ta Dace Magance Matsalar Ba
Published: 24th, May 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa Iran bata amince da kafa kasashe biyu a matsayin hanyar warware rikicin Falasdinawa ba, saboda kafa kasashe biyu ba zai bawa Falasdinawa hakkinsu ba saboda matukar akwai ikon da HKI take da shi a yakin Falasdinawa ba zasu taba samun hakkinsu ba.
Bil’hasali ma kasashe biyu a fahintar mu zai kara wahalar da Falasdinawa ne fiye da hadda suke sha a halin yanzu.
Ministan ya bayyana haka ne a lokacinda ya kai ziyara birnin Vatikan na kasar Italiya inda ya gana da Cardinal Pietro Parolin a jiya Jumma’a. Aragchi ya kara da cewa an dade ana maganar raba gardamar ta hanyar kasashen biyu. Al-hali ba wanda ya amince da kafa kasashen biyu tsakanin yahudawan da kuma mafi yawan Falasdinawa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sojojin Yemen Sun Kai Wa Filin Jirgin Saman “Ben Gorion” Hari Sau Biyu A Yau Alhamis
A karo na biyu sojojin kasar Yemen sun sanar da kai hari akan filin saukar jirgin sama na “Ben Gorion” a matsayin ci gaba da taimakawa Falasdinawa da sojojin HKI suke yi wa kisan kiyashi.
Sanarwar ta sojojin na Yemen ta kuma ce; Makami mai linzamin da su ka harba, wanda ya fi sauti sauri ne, kuma ya sauka a inda aka harba shi, wato filin jiragen sama na Yafa dake karkashin mamaya, da ake kira da “Ben Gorion.”
Harin ya tilastawa miliyoyin ‘yan sahayoniya guduwa zuwa Mabuya sanadiyyar gittawar makami mai linzamin da aka harbo daga kasar Yemen. Haka nan kuma an dakatar da zirga-zirgar jirage a filin na Ben Gorion.
Da safiyar yau ma dai kakakin sojan kasar ta Yemen Janar Yahya Sari, ya sanar da harba makami mai linzamin zuwa Tel Aviv, da kuma jiragen sama marasa matuki zuwa tashar jiragen ruwa na Haifa.
Janar Sari ya tabbatar da cewa sojojin na Yemen za su ci gaba da kai hare-haren nasu akan HKI har zuwa lokacin da za a dakatar da yakin Gaza.