Aminiya:
2025-07-08@15:09:55 GMT

Kwamishinoni: Ku koma APC ko ku yi murabus – Gwamna Eno

Published: 24th, May 2025 GMT

Gwamnan Jihar Akwa Ibom, Fasto Umo Eno, ya bayyana shirinsa na ficewa daga Jam’iyyar PDP zuwa APC, inda ya umarci duka Kwamishinoninsa da sauran masu riƙe da muƙaman siyasa da su sauya sheƙa tare da shi ko kuma su sauka daga muƙamansu.

Da yake bayani a Uyo babban birnin jihar ranar Alhamis, gwamnan ya ce ba zai yi aiki da waɗanda ya naɗa su, su yi aiki da wata jam’iyya ba.

An kama yarinya kan kashe jariri a sansanin ’yan gudun hijira Sojoji sun kashe mayaƙan ISWAP 16 a Borno

Gwamna Eno ya bayyana cewa Jam’iyyar PDP ba ta da taswirar da za ta tabbatar masa da tafiyarsa cikin kwanciyar hankali a zaɓuka, yana mai cewa yana da yaƙinin cewa zai ci zabe a ƙarƙashin kowace jam’iyya saboda ya yi aiki tuƙuru.

Ya bayyana cewa, ya koma Jam’iyyar APC ne saboda ya yi imani da gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu, kuma ba zai iya ci gaba da zama a Jam’iyyar PDP da goyon bayan shugaban Ƙasa kamar yadda Nyesome Wike yake yi a halin yanzu.

Gwamna Eno ya ce duk da yana ƙaunar PDP, ba ya hango nasarar jam’iyyar a zaɓuka masu zuwa, sakamakon rigingimun da jam’iyyar ke ciki.

“Ina son PDP, kuma ina son zama a cikinta, amma a bayyane take ƙarara cewa babu wani ma’auni da zan iya auno wa kaina nasara a zaɓukan da ke tafe..,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: a Jam iyyar

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

Ibrahim ya bayyana cewa, sun rarraba mukamai na rikon jam’iyyar a tsakaninsu, kafin babban taro na kasa a nan gaba.

Gwamnan Jihar Kaduna, Nasiru El-Rufai ya tabbatar cewa; hadakar ta ADC, ta zabi Aregbesola a matsayin sakatarenta na kasa na riko, har ma ya wallafa a jawabin karbar mukamin da ya yi a shafukan sada zumunta.

Matakin ‘yan adawar na shiga ADC, na zuwa ne bayan kasa cimma bukatarsu ta yi wa sabuwar kungiyar mai suna ‘All Democratic Alliance’ (ADA), rajista a matsayin jam’iyyar siyasa, sakamakon jan kafa da suka rika samu daga babbar hukmar zabe ta kasa (INEC).

Haka zalika, Atiku Abubakar da wasu manyan jam’iyar PDP, sun nemi ‘yan jam’iyyar da su hada hannu da su wajen shiga hadakar ta ADC, domin kalubalantar gwamnatin Bola Ahmed Tinubu a shekarar 2027 mai zuwa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ASUU Ta Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Biya Albashin Watan Yuni
  • HKI Tana Tana Son Ci Gaba Da Yaki Kuma Trump Yana Tare Da Shi
  • Lauyoyin Majalisar Dattawan Nijeriya Sun Ƙaryata Natasha Kan Cewa Kotu Ta Ce Ta Koma Bakin Aiki
  • Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC
  • Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum
  • Ranar Talata Mai Zuwa Zan Koma Zauren Majalisar Dattawa – Sanata Natasha
  • Gwamna ya gargaɗi sarakuna kan mamaye filayen kiwo a Gombe
  • Imam Khaminae Ya Halarci Makokin Ashoora A Gidansa A Tehran
  • ‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027
  • Kwankwaso ba zai yi mana takara a 2027 ba — NNPP