Eslami : duk wani mataki da Iran ta dauka ya dogara ne kan manufofi da muradun kasar
Published: 24th, May 2025 GMT
Shugaban Hukumar Makamashin Nukiliya ta Iran (AEOI) Mohammad Eslami ya ce duk wanimataki da Tehran ta dauka ya dogara ne kan manufofi da muradun kasar.
“Muna ci gaba bisa ga manufofinmu da bukatun kasa,” in ji Eslami
Babban jami’in nukiliya na kasar Iran ya jaddada cewa daya daga cikin muhimman nasarorin juyin juya halin Musulunci shi ne yadda kasar ke tsara tafarkinta da kuma yanke hukunci bisa muradun kasa.
Eslami ya bayyana cewa, a halin yanzu Iran tana matsayi mai kyau a fannin kimiyya da fasaha na masana’antu, daidai da kasashen da suka ci gaba da suka zuba jarin miliyoyin daloli.
Kafin hakan dama Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei a ranar Talata ya bayyana cewa “ba daidai ba ne” a ce Amurka ta dage kan Iran ta dakatar da ayyukanta na inganta makamashin Uranium cikin lumana.
Jagoran ya ce “Babu wanda ke jiran izini daga wurin kowa, Jamhuriyar Musulunci tana da manufofinta, hanyoyinta, kuma tana aiwatar da manufofinta.”
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ministan Tsaron Kasar venezuela Ya Gargadi Amurka Dangane Da Kokarin Juyin Mulki A Kasar
Ministan tsaro na kasar Venezuela Vladimir Padrino López ya gargadi gwamnatin Amurka dangane da duk wani kokari na kaiwa kasar Venuzuela hare hare saboda kifar da gwamnatin shugaba Nicolas Madoro. Tare da fakewa da fasakorin kwayoyi.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Vladimir yana cewa take-taken gwamnatin Amurka na sojojin da ta kawo a teken carebian ya yi kama da takalar yaki ne da kasar Venezuela , kuma idan haka ne, to sojojin sa a shirye suke su fuskance su, su kumakare kasarsu.
Kamfanin dillancin labaran IP nakasar Iran ya bayyana cewa, Amurka ta fara kai ruwa rana da gwamnatin shugaba Madoro ne tun lokacinda shugaban Amurka Donal Trump ya bayyana shugaban kasar ta Venezuela a matsayin dan kwaya kuma mai fasa korin kwayoyi.
A halin yanzu dai gwamnatin Trump ta tura sojojinta zuwa tekun Carabian kusa da kasar ta Venezuela da nufin kifar da gwamnatin Nicolas Madoro.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila September 16, 2025 Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya September 16, 2025 Bayanin Bayan Taron Doha Ya Yi Kira Da A Kafa Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kare Kai September 15, 2025 Fira Ministan Spain: Bai Kamata A Rika Barin “Isr’ila” Tana Shiga Gasar September 15, 2025 Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Sarkin Kasar Qatar A Birnin Doha September 15, 2025 Dan Kasar Iran Mai Kirkira Ya Sami Kyautar Yabo A Kasar China September 15, 2025 Fizishkiyan: Wajibi Ne Musulmi Su Hada Kai Domin Dakatar Da Laifukan HKI September 15, 2025 Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha September 15, 2025 Kwamitin Kolin Tsron Kasar Iran Ya Amince Da Yarjejeniyar Da Aka Cimma Da Hukumar IAEA September 15, 2025 Jami’in Kasar Yemen Ya Aike Da Sako Ga Mahalarta Taron Birnin Doha Na Kasar Qatar September 15, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci