Eslami : duk wani mataki da Iran ta dauka ya dogara ne kan manufofi da muradun kasar
Published: 24th, May 2025 GMT
Shugaban Hukumar Makamashin Nukiliya ta Iran (AEOI) Mohammad Eslami ya ce duk wanimataki da Tehran ta dauka ya dogara ne kan manufofi da muradun kasar.
“Muna ci gaba bisa ga manufofinmu da bukatun kasa,” in ji Eslami
Babban jami’in nukiliya na kasar Iran ya jaddada cewa daya daga cikin muhimman nasarorin juyin juya halin Musulunci shi ne yadda kasar ke tsara tafarkinta da kuma yanke hukunci bisa muradun kasa.
Eslami ya bayyana cewa, a halin yanzu Iran tana matsayi mai kyau a fannin kimiyya da fasaha na masana’antu, daidai da kasashen da suka ci gaba da suka zuba jarin miliyoyin daloli.
Kafin hakan dama Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei a ranar Talata ya bayyana cewa “ba daidai ba ne” a ce Amurka ta dage kan Iran ta dakatar da ayyukanta na inganta makamashin Uranium cikin lumana.
Jagoran ya ce “Babu wanda ke jiran izini daga wurin kowa, Jamhuriyar Musulunci tana da manufofinta, hanyoyinta, kuma tana aiwatar da manufofinta.”
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kakakin Rundunar Izzuddeen Qassam ya Bayyana Yadda Suka Yi Kofar Rago Ga Sojojin Mamayar Isra’ila
Kakakin dakarun rundunar Izzudden-Qassam ya bayyan cewa: ‘Yan gwagwarmaya sun tarwatsa wani mutum-mutumi da sojojin mamayar Isra’ila suka makare da harsashai dauke da makami mai linzami a lokacin da ake shirya shi
A cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na Twitter, kakakin rundunar sojin Qassam bangaren sojin kungiyar Hamas Abu Obeida, ya yi bayyana cewa: ‘yan gwagwarmaya sun nuna jarumtaka wajen tunkarar makircin ‘yan mamaya mai sarkakiya a gwagwarmayar Beit Hanoun, inda suka kara raunana martabar sojojin mamaya tare da rusa makircinsu..
Kakakin rundunar sojin Qassam Abu Obeida, ya kara da cewa: Hadadden aikin na Beit Hanoun wani karin mataki ne da ‘yan gwagawarmaya suka dauka na raunana makiya tare da rusa martabar sojojin mamayar Isra’ila.
Yana mai jaddadad cewa: Yakin da ‘yan gwagwarmaya ke yi da makiya daga arewacin Zirin Gaza zuwa kudancinta, zai kara haifar da hasara ga ‘yan mamaya a kowace rana, kuma ko da kuwa a ‘yan kwanakin nan sun samu nasarar kubutar da dakarunsu gwagwarmaya daga wani makircin ‘yan mamaya tare da killace sojojin mamayar Isra’ila da haka ya Sanya suka kara kama fursunonin yaki.