A yau Juma’a, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya tattauna ta wayar tarho da shugaban gwamnatin kasar Jamus Friedrich Merz, bisa gayyatarsa da aka yi.

Xi Jinping ya jaddada cewa, Sin da Jamus suna raya dangantakar dake tsakaninsu bisa girmama juna, da amincewa da bambance-bambance, da hadin gwiwa don samun moriyar juna, kuma akwai bukatar bangarorin biyu su yi kokari tare don tabbatar da raya dangantakarsu yadda ya kamata.

Ya ce, da farko dai, ya kamata a yi imani da juna a fannin siyasa tsakanin kasashen biyu. Na biyu kuma, ya kamata a kara inganta dangantakarsu, wato ci gaba da hadin gwiwa a fannonin da suka riga sun hada hannu kamar su kera motoci, da injuna, da kuma masana’antar sinadarai da kuma kara fadada hadin gwiwarsu a sabbin fannoni kamar fasahar AI, da fasahar quantum da sauransu. Na uku kuma, ya kamata a kara karfi wajen hadin gwiwarsu, watau Sin tana fatan kasar Jamus za ta kara samar da goyon baya da sauki da gabatar da manufofi don inganta zuba jari da hadin gwiwar dake tsakanin kasashen biyu, ta yadda za a samar da yanayin cinikayya mai adalci da daidaito da gudanar da komai a bude, ga kamfanonin kasar Sin.

A nasa bangare, Merz ya bayyana cewa, sabuwar gwamnatin kasar Jamus za ta ci gaba da tsayawa tsayin daka kan manufar Sin daya tak a duniya, da kokarin raya dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare a tsakanin kasashen biyu bisa halin da ake ciki yadda ya kamata. Har ila yau, ya ce kasar Jamus tana begen kara mu’amala da hadin gwiwa da kasar Sin, da bude kofarta ga kasashen waje da samun moriyar juna, da sa kaimi ga yin ciniki cikin adalci, da tabbatar da zaman lafiya a duniya, da kuma tinkarar kalubalen duniya kamar sauyin yanayi tare. (Zainab Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: kasar Jamus

এছাড়াও পড়ুন:

Turji: Sai ka sako mutanen da ka sace za a yi sulhu — Gwamnatin Sakkwato

Gwamnatin Jihar Sakkwato ta ƙalubalanci jagoran ’yan bindiga Bello Turji, wanda ke neman sulhu, da cewa idan da gaske yake yi, to ya sako duk mutanen da ya yi garkuwa da su, ya daina kai hare-hare, kafin ta zauna da shi.

Mashawarci na musamman ga gwamnan Sakkwato a kan sha’anin tsaro, Kanar Ahmed Usman ne ya bayyana hakan baya yaɗuwar wani bidiyo da Turji ya saki, wanda a ciki yake neman a yi tsakaninsa da gwamnati.

Ɗan ta’addan wanda ya addabi yankunan jihar da makwabta ya saki bidiyon ne kwanaki kaɗan bayan jami’an tsaro sun kashe wasu gaggan kwamandojinsa da Faransa sama da 100.

Kamar Ahmed, a cikin wata sanarwa ya bayyana cewa babu yadda za a tabbatar cewa neman sulhun Turji ba ta fatar baki ba ne, sai idan ya dakatar da kai wa al’ummo hare-hare saki duk mutanen da ya sace ba tare da ɓata lokaci ba.

Bincike ya nuna ’yan Najeriya ba su gamsu da gwamnatin Tinubu ba Mutum 21 sun rasu a hatsarin mota a kan hanyar Zariya–Kano NAJERIYA A YAU: Mene ne tasirin naɗin Mataimaka na Musamman a rayuwar jama’a?

“Idan har da gaske yana neman sulhu, to sai ya nuna a aikace, ya dakatar da hare-hare kan ƙauyuka tare da sakin duk mutanen da ke hannunsa ba tare da sharaɗi ba,” in ji Kanar Ahmed, wanda ke jaddada muhimmancin tsaron rayuka da lafiyar da kuma dukiyoyin al’umma ga gwamnatin Jihar Sakkwato.

Don haka ya, “Ba za a iya yin wata sahihiyar tattaunawar sulhu da za a yi a samu a yayin al’ummomi suke zaune cikin tsoro kuma ’yan ta’adda suke yin garkuwa da mutane.

“Matakin farko na samun zaman lafiya shi ne gina yarda ta hanyar ɗaukar ƙwararan matakai a aikace,” in ji jami’in gwmanatin.

Ya jaddada aniyar gwamnatin ga tabbatar da tsaro da zaman lafiya, amma ba za ta lamunci ta’addancibda sauran miyagun laifuka ba.

Sa’annan ya yi kira ga al’ummomi da shugabannin addini da sarakunan gargajiya da ƙungiyoyin faren hula su mara wa shirye-shiryen zaman lafiya baya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar China Ta Yi Watsi da Barazanar Trump Na Kakabawa Kasashen BRICS Karin Takunkuman Tattalin Arziki
  • Gwamnatin Kasar Iran Ta Yi Allawadai Da Hare-Haren HKI Kan Kasar Yemen
  • Gwamnatin Kasar Iran Ta Yaba Da Kungiyar BRICS Saboda Yin Tir Da HKI A Yakin Kwanaki 12
  • China Ta Maida Martani da Haka Kayakin Kiwon Lafiya Na Tarayyar Turai Shigowa Kasar
  • Turji: Sai ka sako mutanen da ka sace za a yi sulhu — Gwamnatin Sakkwato
  • Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin
  • Shugaban Kasar Iran Ya Ce Kungiyar ECO Ta Yi Tir Da Hare-Haren HKI Kan Kasarsa
  • Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa
  • Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu
  • Kasar Iran Ta Jaddada Wajabcin Hukunta Gwamnatin Mamayar Isra’ila Dangane Da  Ta’addancinta Kan Iran