Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Gwamnatin Jamus Friedrich Merz
Published: 23rd, May 2025 GMT
A yau Juma’a, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya tattauna ta wayar tarho da shugaban gwamnatin kasar Jamus Friedrich Merz, bisa gayyatarsa da aka yi.
Xi Jinping ya jaddada cewa, Sin da Jamus suna raya dangantakar dake tsakaninsu bisa girmama juna, da amincewa da bambance-bambance, da hadin gwiwa don samun moriyar juna, kuma akwai bukatar bangarorin biyu su yi kokari tare don tabbatar da raya dangantakarsu yadda ya kamata.
A nasa bangare, Merz ya bayyana cewa, sabuwar gwamnatin kasar Jamus za ta ci gaba da tsayawa tsayin daka kan manufar Sin daya tak a duniya, da kokarin raya dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare a tsakanin kasashen biyu bisa halin da ake ciki yadda ya kamata. Har ila yau, ya ce kasar Jamus tana begen kara mu’amala da hadin gwiwa da kasar Sin, da bude kofarta ga kasashen waje da samun moriyar juna, da sa kaimi ga yin ciniki cikin adalci, da tabbatar da zaman lafiya a duniya, da kuma tinkarar kalubalen duniya kamar sauyin yanayi tare. (Zainab Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: kasar Jamus
এছাড়াও পড়ুন:
Turji: Sai ka sako mutanen da ka sace za a yi sulhu — Gwamnatin Sakkwato
Gwamnatin Jihar Sakkwato ta ƙalubalanci jagoran ’yan bindiga Bello Turji, wanda ke neman sulhu, da cewa idan da gaske yake yi, to ya sako duk mutanen da ya yi garkuwa da su, ya daina kai hare-hare, kafin ta zauna da shi.
Mashawarci na musamman ga gwamnan Sakkwato a kan sha’anin tsaro, Kanar Ahmed Usman ne ya bayyana hakan baya yaɗuwar wani bidiyo da Turji ya saki, wanda a ciki yake neman a yi tsakaninsa da gwamnati.
Ɗan ta’addan wanda ya addabi yankunan jihar da makwabta ya saki bidiyon ne kwanaki kaɗan bayan jami’an tsaro sun kashe wasu gaggan kwamandojinsa da Faransa sama da 100.
Kamar Ahmed, a cikin wata sanarwa ya bayyana cewa babu yadda za a tabbatar cewa neman sulhun Turji ba ta fatar baki ba ne, sai idan ya dakatar da kai wa al’ummo hare-hare saki duk mutanen da ya sace ba tare da ɓata lokaci ba.
Bincike ya nuna ’yan Najeriya ba su gamsu da gwamnatin Tinubu ba Mutum 21 sun rasu a hatsarin mota a kan hanyar Zariya–Kano NAJERIYA A YAU: Mene ne tasirin naɗin Mataimaka na Musamman a rayuwar jama’a?“Idan har da gaske yana neman sulhu, to sai ya nuna a aikace, ya dakatar da hare-hare kan ƙauyuka tare da sakin duk mutanen da ke hannunsa ba tare da sharaɗi ba,” in ji Kanar Ahmed, wanda ke jaddada muhimmancin tsaron rayuka da lafiyar da kuma dukiyoyin al’umma ga gwamnatin Jihar Sakkwato.
Don haka ya, “Ba za a iya yin wata sahihiyar tattaunawar sulhu da za a yi a samu a yayin al’ummomi suke zaune cikin tsoro kuma ’yan ta’adda suke yin garkuwa da mutane.
“Matakin farko na samun zaman lafiya shi ne gina yarda ta hanyar ɗaukar ƙwararan matakai a aikace,” in ji jami’in gwmanatin.
Ya jaddada aniyar gwamnatin ga tabbatar da tsaro da zaman lafiya, amma ba za ta lamunci ta’addancibda sauran miyagun laifuka ba.
Sa’annan ya yi kira ga al’ummomi da shugabannin addini da sarakunan gargajiya da ƙungiyoyin faren hula su mara wa shirye-shiryen zaman lafiya baya.