A yau Juma’a, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya tattauna ta wayar tarho da shugaban gwamnatin kasar Jamus Friedrich Merz, bisa gayyatarsa da aka yi.

Xi Jinping ya jaddada cewa, Sin da Jamus suna raya dangantakar dake tsakaninsu bisa girmama juna, da amincewa da bambance-bambance, da hadin gwiwa don samun moriyar juna, kuma akwai bukatar bangarorin biyu su yi kokari tare don tabbatar da raya dangantakarsu yadda ya kamata.

Ya ce, da farko dai, ya kamata a yi imani da juna a fannin siyasa tsakanin kasashen biyu. Na biyu kuma, ya kamata a kara inganta dangantakarsu, wato ci gaba da hadin gwiwa a fannonin da suka riga sun hada hannu kamar su kera motoci, da injuna, da kuma masana’antar sinadarai da kuma kara fadada hadin gwiwarsu a sabbin fannoni kamar fasahar AI, da fasahar quantum da sauransu. Na uku kuma, ya kamata a kara karfi wajen hadin gwiwarsu, watau Sin tana fatan kasar Jamus za ta kara samar da goyon baya da sauki da gabatar da manufofi don inganta zuba jari da hadin gwiwar dake tsakanin kasashen biyu, ta yadda za a samar da yanayin cinikayya mai adalci da daidaito da gudanar da komai a bude, ga kamfanonin kasar Sin.

A nasa bangare, Merz ya bayyana cewa, sabuwar gwamnatin kasar Jamus za ta ci gaba da tsayawa tsayin daka kan manufar Sin daya tak a duniya, da kokarin raya dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare a tsakanin kasashen biyu bisa halin da ake ciki yadda ya kamata. Har ila yau, ya ce kasar Jamus tana begen kara mu’amala da hadin gwiwa da kasar Sin, da bude kofarta ga kasashen waje da samun moriyar juna, da sa kaimi ga yin ciniki cikin adalci, da tabbatar da zaman lafiya a duniya, da kuma tinkarar kalubalen duniya kamar sauyin yanayi tare. (Zainab Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: kasar Jamus

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Nasarorin Noma da Tsaron Abinci Karkashin Shirin Renewed Hope

 

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta bayyana muhimman nasarori da ta cimma a fannin noma da tabbacin isasshen abinci, karkashin shirin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na Renewed Hope.

Rahoton rabin wa’adi na aiki daga watan Mayu 2023 zuwa Afrilu 2025, wanda Ofishin Mai Baiwa Shugaban Kasa Shawara kan Tsare-Tsare da Hadin Gwiwa ya fitar, ya bayyana ayyukan da Ma’aikatar Noma da Tsaron Abinci ta gudanar domin cika alkawurran yakin neman zaben shugaban kasa.

Daya daga cikin manyan nasarorin da aka samu a rahoton shi ne sabunta da inganta dakunan ajiya na abinci na kasa, wanda ya taimaka wajen rage karancin abinci da daidaita farashi a kasuwanni.

Ma’aikatar ta kuma kaddamar da ayyukan gina hanyoyin ban ruwa da tafkunan ruwa domin kara yawan amfanin gona a duk shekara. Bugu da kari, an gudanar da shirin share filaye masu fadi domin kara yawan filayen noma.

A wani bangare, gwamnati ta aiwatar da shirye-shiryen musamman domin tallafawa matasa da mata masu sha’awar harkar noma. An hada da horaswa, tallafin kudi, da samar da hanyoyin samun abinci da kudin shiga ga iyalai, domin rage fatara da bunkasa yankunan karkara.

Haka kuma, an mayar da hankali wajen tabbatar da cewa kayan gona na fitar kasashen waje sun cika ka’idojin lafiya da inganci na duniya. Wannan ya baiwa Najeriya damar kara samun kudin shiga daga fitar da amfanin gona.

Ma’aikatar ta kuma karfafa aiwatar da muhimman sassa na shirin National Livestock Transformation Plan (NLTP) da ke karkashinta, wanda ya hada da samar da wuraren kiwo, shuka ciyayi da kula da dabbobi. Wannan ya taimaka wajen rage rikice-rikice tsakanin manoma da makiyaya da kuma kara yawan kiwo.

Rahoton ya nuna cewa nasarorin da aka samu sun yi daidai da alkawurran da Shugaba Tinubu ya dauka a lokacin yakin neman zabe, inda ya yi alkawarin tabbatar da wadatar abinci da bunkasar tattalin arzikin kasa ta hanyar noma.

Jami’an gwamnati sun jaddada cewa za su ci gaba da aiwatar da shirye-shiryen da za su karfafa bangaren noma, su samar da ayyukan yi, da kuma bunkasa rayuwar al’umma.

Bello Wakili

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Bukaci Kada Amurka Ta Siyasantar Da Hadin Gwiwar Bangaren Ilimi
  • Kungiyar Ta’addanci Ta ISIS Ta Zargi Shugaban Gwamnatin Siriya Da Kauce Hanya Madaidaiciya
  • Yan Majalisar Tarayya Na Katsina Sun Mara Wa Gwamna Dikko Radda Baya Don Takarar Zango Na Biyu
  • Masanan Najeriya Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwar Afirka Da Sin A Fannin Tinkarar Kalubalen Harajin Kwastam Na Amurka
  • Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Faransa
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Nasarorin Noma da Tsaron Abinci Karkashin Shirin Renewed Hope
  • Yakin Gaza : Tarayyar Turai za ta sake nazari kan Yarjejeniyarta da Isra’ila
  • Salon “Kasa Daya Manufa Daya” Ya Dace Da “Ayyuka Goma” Na Hadin Gwiwa Da Afirka
  • An Tattauna Hanyar Zamanantar Da Kasa A Dandalin Tattaunawa Na Masanan Sin Da Afirka