Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Gwamnatin Jamus Friedrich Merz
Published: 23rd, May 2025 GMT
A yau Juma’a, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya tattauna ta wayar tarho da shugaban gwamnatin kasar Jamus Friedrich Merz, bisa gayyatarsa da aka yi.
Xi Jinping ya jaddada cewa, Sin da Jamus suna raya dangantakar dake tsakaninsu bisa girmama juna, da amincewa da bambance-bambance, da hadin gwiwa don samun moriyar juna, kuma akwai bukatar bangarorin biyu su yi kokari tare don tabbatar da raya dangantakarsu yadda ya kamata.
A nasa bangare, Merz ya bayyana cewa, sabuwar gwamnatin kasar Jamus za ta ci gaba da tsayawa tsayin daka kan manufar Sin daya tak a duniya, da kokarin raya dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare a tsakanin kasashen biyu bisa halin da ake ciki yadda ya kamata. Har ila yau, ya ce kasar Jamus tana begen kara mu’amala da hadin gwiwa da kasar Sin, da bude kofarta ga kasashen waje da samun moriyar juna, da sa kaimi ga yin ciniki cikin adalci, da tabbatar da zaman lafiya a duniya, da kuma tinkarar kalubalen duniya kamar sauyin yanayi tare. (Zainab Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: kasar Jamus
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Nasarorin Noma da Tsaron Abinci Karkashin Shirin Renewed Hope
Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta bayyana muhimman nasarori da ta cimma a fannin noma da tabbacin isasshen abinci, karkashin shirin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na Renewed Hope.
Rahoton rabin wa’adi na aiki daga watan Mayu 2023 zuwa Afrilu 2025, wanda Ofishin Mai Baiwa Shugaban Kasa Shawara kan Tsare-Tsare da Hadin Gwiwa ya fitar, ya bayyana ayyukan da Ma’aikatar Noma da Tsaron Abinci ta gudanar domin cika alkawurran yakin neman zaben shugaban kasa.
Daya daga cikin manyan nasarorin da aka samu a rahoton shi ne sabunta da inganta dakunan ajiya na abinci na kasa, wanda ya taimaka wajen rage karancin abinci da daidaita farashi a kasuwanni.
Ma’aikatar ta kuma kaddamar da ayyukan gina hanyoyin ban ruwa da tafkunan ruwa domin kara yawan amfanin gona a duk shekara. Bugu da kari, an gudanar da shirin share filaye masu fadi domin kara yawan filayen noma.
A wani bangare, gwamnati ta aiwatar da shirye-shiryen musamman domin tallafawa matasa da mata masu sha’awar harkar noma. An hada da horaswa, tallafin kudi, da samar da hanyoyin samun abinci da kudin shiga ga iyalai, domin rage fatara da bunkasa yankunan karkara.
Haka kuma, an mayar da hankali wajen tabbatar da cewa kayan gona na fitar kasashen waje sun cika ka’idojin lafiya da inganci na duniya. Wannan ya baiwa Najeriya damar kara samun kudin shiga daga fitar da amfanin gona.
Ma’aikatar ta kuma karfafa aiwatar da muhimman sassa na shirin National Livestock Transformation Plan (NLTP) da ke karkashinta, wanda ya hada da samar da wuraren kiwo, shuka ciyayi da kula da dabbobi. Wannan ya taimaka wajen rage rikice-rikice tsakanin manoma da makiyaya da kuma kara yawan kiwo.
Rahoton ya nuna cewa nasarorin da aka samu sun yi daidai da alkawurran da Shugaba Tinubu ya dauka a lokacin yakin neman zabe, inda ya yi alkawarin tabbatar da wadatar abinci da bunkasar tattalin arzikin kasa ta hanyar noma.
Jami’an gwamnati sun jaddada cewa za su ci gaba da aiwatar da shirye-shiryen da za su karfafa bangaren noma, su samar da ayyukan yi, da kuma bunkasa rayuwar al’umma.
Bello Wakili