HausaTv:
2025-05-24@14:35:14 GMT

SojojinHKI Sun Kashe Akalla Mutane 75 A Gaza A Ranar Jumma’a Kadai

Published: 24th, May 2025 GMT

Sojojin HKI sun sabonta hare-hare a ranar Jumma’a kan fararen hula a kan Falasdinawa a Gaza, inda suka kashe akalla mutane 76 ajiya jumma’a kadai sannan wasu dadama suka ji rauni.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto majiyar Falasdinawa a Gaza na cewa sojojin HKI sun kai hare-hare a kan wani gida a Khan Yunus inda suka kashe akalla mutane.

A wani  harin da sojojin yahudawan suka kai khan yunus har’ila yau ya kashe falasdinawa akalla 8.

Alaa Al-Najjar, likita a asbitin Nasir ya bayyana cewa ta rasa yayanta har 9 a cikin asbitin sanadiyyar hare-haren HKI a kan shi.

Harin da yahudawan suka kai kan gidan Annajjar dai ya rusa gidan daga sama har kasa sannan wutan da ya taso daga gidan sai da ya watsu zuwa gidajen da suke makobtaka da gidan nata.

Dr Annajjar ta sami labarin hari a kan gidanta ne a lokacinda take aiki a kan wasu kananan yara. Yayanta sun kama daga shekara 2-16. Sannan mijinta na daga cikin wadanda suka ji rauni.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun kashe mayaƙan ISWAP 5 a Borno

Dakarun sojin Najeriya sun kashe mayakan kungiyar ISWAP guda biyar sa’annan suka fatattaki ragowar da suka kawo hari a sansanin soji da ke kauyen Gajibo da ke Karamar Hukumar Dikwa a Jihar Borno.

Wata majiyar daga Zagàzola makama na cewar, ’yan ta’addan sun kai hari kauyen Gajibo ne da misalin karfe 10:20 na daren ranar alhamis, inda sojojin rundunar Operation Hadin Kai suka yi musayar wata da su suka fatattaki maharan da hadin gwiwar dakarun rundunar ta 134 da suka isa garin.

A yayin arangamar ’yan ta’addan sun tsere sun bar nau’uka daban-daban na makamai da suka hada da kuma na’urar sadarwa.

Rundunar sojin Najeriya na ci gaba da jajircewa wajen ganin ta kawar da ta’addanci, musamman bisa la’akari da yawaitar hare-haren ’yan ta’addan da suka zafafa a kwanan nan a yankin Arewa Maso Gabasa.

Mace ta damfari masu neman aikin gwamnati Naira miliyan 250 An kama yarinya kan kashe jariri a sansanin ’yan gudun hijira

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji sun kashe mayaƙan ISWAP 5 a Borno
  • A Yemen An Yi Gangamin Miliyoyin Mutane Na Nuna Goyon Bayan Falasdinawa
  • Sojoji sun kashe mayaƙan ISWAP 16 a Borno
  • Sojoji sun kashe mayaƙan ISWAP 16 a Bormo
  • Sojoji Sun Kashe Ƴan Boko Haram 16 A Borno Bayan Sun Kawo Hari Barikinsu
  • Limamin Masallacin Jumma’a A Nan Tehran Ya Yi Magana Dangane Da Kwatar Garin Khurramshar Daga Sojojin Sadam
  • Zargin Satar Fasaha: Kotu ta sanya ranar yanke hukunci kan shari’ar BBC
  • Rashin Tsaro: Matasa Sun Yi Zanga-zangar Toshe Babbar Hanya Saboda Satar Mutane A Edo
  • Ma’aikatan wutar lantarki sun tsunduma yajin aiki a Kano