SojojinHKI Sun Kashe Akalla Mutane 75 A Gaza A Ranar Jumma’a Kadai
Published: 24th, May 2025 GMT
Sojojin HKI sun sabonta hare-hare a ranar Jumma’a kan fararen hula a kan Falasdinawa a Gaza, inda suka kashe akalla mutane 76 ajiya jumma’a kadai sannan wasu dadama suka ji rauni.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto majiyar Falasdinawa a Gaza na cewa sojojin HKI sun kai hare-hare a kan wani gida a Khan Yunus inda suka kashe akalla mutane.
Alaa Al-Najjar, likita a asbitin Nasir ya bayyana cewa ta rasa yayanta har 9 a cikin asbitin sanadiyyar hare-haren HKI a kan shi.
Harin da yahudawan suka kai kan gidan Annajjar dai ya rusa gidan daga sama har kasa sannan wutan da ya taso daga gidan sai da ya watsu zuwa gidajen da suke makobtaka da gidan nata.
Dr Annajjar ta sami labarin hari a kan gidanta ne a lokacinda take aiki a kan wasu kananan yara. Yayanta sun kama daga shekara 2-16. Sannan mijinta na daga cikin wadanda suka ji rauni.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ranar Talata Mai Zuwa Zan Koma Zauren Majalisar Dattawa – Sanata Natasha
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp