Aminiya:
2025-05-01@04:38:46 GMT

Majalisun Tarayya sun amince da kasafin kuɗin N54.9trn na 2025

Published: 13th, February 2025 GMT

Majalisar Dattawa da ta Wakilai, sun amince da kasafin kuɗin shekarar 2025 wanda ya kai Naira Tiriliyan 54.9.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ne, ya gabatar da kasafin kuɗin, inda aka duba shi dalla-dalla kafin a amincewa da shi.

Kwastam ta lalata magungunan biliyan N100 a Ribas An yanke hukuncin sare hannun matashi kan sare hannun yaro a Gombe

A majalisar wakilai, ’yan majalisa sun yi nazari kan kasafin kuɗin mataki-mataki kafin su amince da shi a ranar Alhamis.

Shugaban kwamitin kasafin kuɗi na majalisar, Hon. Abubakar Kabir Abubakar Bichi ne, ya gabatar da shi a zaman majalisar.

Bayan tattaunawa da kwamitocin majalisar, an kaɗa ƙuri’ar amincewa da kasafin kuɗin ƙarƙashin jagorancin Kakakin Majalisar, Abbas Tajuddeen.

Sabon kasafin kuɗin ya ƙunshi kuɗaɗen da aka ware wajen doka, biyan bashi, ayyukan gwamnati, da kuma manyan ayyukan raya ƙasa.

A ɓangaren majalisar dattawa, an amince da kasafin kuɗin bayan rahoton da kwamitin kasafin kuɗi ya gabatar, wanda Sanata Solomon Olamilekan Adeola ke jagoranta.

Bayan kammala karanta takardar kasafin kuɗin, Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya karanta cikakkun bayanai kafin a kaɗa ƙuri’a.

Sanata Opeyemi Bamidele ne, ya gabatar da ƙudirin amincewa da kasafin kuɗin karo na uku, inda Sanata Abba Moro ya mara masa baya.

Bayan amincewa da kasafin kuɗin, gwamnati ta bayyana yadda za a kashe kuɗaɗe a shekarar 2025, inda za a mayar da hankali kan ci gaban tattalin arziƙi, manyan ayyuka, da walwalar al’umma.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan majalisa Amincewa Majalisar Dattawa Majalisar Wakilai amincewa da

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Tarayya ta ayyana hutu gobe Alhamis

Gwamnatin Nijeriya ta ayyana gobe Alhamis 1 ga watan Mayu a matsayin ranar hutu ga ma’aikatan ƙasar albarkacin bikin murnar Ranar Ma’aikata ta Duniya.

Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa da Ministan Harkokin Cikin Gida na ƙasar, Olubunmi Tunji-Ojo, ya fitar a yammacin wannan Larabar.

AU ta janye takunkumin da ta ƙaƙaba wa Gabon Tsoffin ma’aikatan NECO na neman a biya su bashin haƙƙoƙinsu

Sanarwar ta ambato ministan yana yaba wa ma’aikatan ƙasar kan sadaukarwa da jajircewar da suke yi wajen gudanar da ayyukansu.

Ministan ya kuma yaba musu kan gudunmawar da suke bayarwa wajen ciyar da Nijeriya gaba.

Ana dai gudanar da bikin Ranar Ma’aikata a ranar 1 ga watan Mayun kowace shekara a sassan duniya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Tarayya ta ayyana hutu gobe Alhamis
  • Gwamnan Sokoto Ya Amince Da Sauya Wa Manyan Sakatarori 25 Ma’aikatu A Jihar 
  • Dokta Bashir ya zama shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci ta Nijeriya
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Na Iran Ya Ce: Maganar ‘Yan Sahayoniyya Rudu Ne Maras Amfani
  • Shugaban Majalisar Ƙoli ta Shari’ar Musulunci a Najeriya ya rasu
  • Har Yanzun Ana Zaman Dar-Dar A Burkina Faso Bayan Kokarin Juyin Mulkin Da Bai SamiNasara Ba
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Jaddada Wajabcin Komawa Kan Shirin Tsagaita Bude Wuta A Gaza
  • Gwamnatin Tarayya Ta Umurci WAEC, NECO Su Koma Amfani Da CBT Nan Da 2026
  • Falasdinu: Mahmud Abbas Ya Nada Magaji Da Kuma Mataimakasa
  • Al-Shara Ya Ki Abincikewa Da Tsarin Tarayya Wanda Kurdawan Kasar Siriya  Suke Bukata