Saudiya Ta Bukaci A Kafa Kasar Falasdinu Don Kawo Karshen Rigima A Gabas Ta Tsakiya
Published: 24th, May 2025 GMT
Gwamnatin kasar Saudiya ta bukaci a amince da samuwar kasar Falasdinu mai zamanta ne kawai hanyar warware rikicin gabas ta tsakiya.
Shafin yanar gizo na labarai Arabnews na kasar Saudiya ya nakalto majiyar Saudia na fadar haka a MDD a jiya Jumma’a. Ta kuma kara da cewa Falasdinawa ba zasu taba amincewa a koresu daga kasarsu ba kamar yadda wasu yahudawa da magoya bayansu suke so.
Labarin ya kara da cewa wannan bukatar na zuwa ne a dai-dai kasashen ta Saudia da Faransa suke kokarin gudanar da gagarumin Taro a cikin watan Yuni mai zuwa don bunkasa wannan ra’ayin ta kafa kasashe biyu.
Wannan ra’ayin yana kara samun goyon baya a wannan makon musamman bayan da HKI ta kara yawan kissan da takewa Falasdinawa a Gaza, wadanda suka ki barin kasarsu zuwa ko ina a duniya.
Manal Radwan daga ma’aikatar harkokin wajen kasar Saudiya wacce kuma take daga cikin wadanda suke shirin taron na NewYork ta fadawa majalisar kan cewa matsalolin rikicin falasdinawa da HKI suna da dama amma mafi muhimmanci daga cikinsu shi ne rashin amincewa da samuwar juna.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
NAJERIYA A YAU: Sarkakiyar Dake Gaban Hadakar ADC — Atiku Ko Peter Obi
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
‘Yan Najeriya suna ci gaba da tafka muhawara a kan wanda jamiyyar hadaka ta ADC zata tsayar takarar Shugaban Kasa a zaben 2027.
Yayin da wasu suke ganin Atiku Abubakar yana da dimbin magoya baya, wasu kuwa gani suke yi shi ma Peter Obi ba kanwar lasa bane.
Ko me zai faru idan daya daga cikin su ya samu tikitin tsayawa takara a 2027?
NAJERIYA A YAU: Mene ne tasirin naɗin Mataimaka na Musamman a rayuwar jama’a? DAGA LARABA: Cutukan Da Sinadaran Yin Burodi Ke HaifarwaShirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne a kan wannan lamari.
Domin sauke shirin, latsa nan