Ministan ya kuma zayyano jerin shirye-shiryen da gwamnatin tarayya ta kirkiro da nufin zaburar da matasa rungumar kiwon dabbobi, musamman don samun riba ciki har da sama musu hektar noma 51,000, a karkashin hadaka da shirin fitar da kaya na ‘Gulf’ na jihohi da kuma shirye-shiryen farfado da guraren kiwon dabbobi 417 a daukacin fadin kasar nan.

“Muna da abubuwan da za mu yi amfani da su a kasar nan, domin yakar yunwa a fadin kasar baki-daya,” in ji Ministan.

“Akalla a kasar nan, muna da Shanu kimanin miliyan sha biyar da Tumakai miliyan 60 da Kaji da miliyan 600 da Akuyoyi da miliyan 1.4 da Rakuma miliyan 700,000 tare kuma da kasar noma, amma sai dai har yanzu, kasar na shigowa da Madarar Shanu,” in ji shi.

“Wannan wata dama ce, domin abin da muke bukata shi ne, sanya wa matasan kasar karsashin rungumar kiwon dabbobi, domin samun riba,“ in ji Ministan.

Mukhtar ya kuma kalubalanci matasan kasar nan da su yi amfani da fasahar zamani wajen kiwon dabbobin, musamman domin cike gibin noman gargajiyar da ake da shi.

“Ya zame mana wajibi a yanzu a wannan fanni na kimiyya da fasaha, mu kawar da amfani da kayan aikin noma na gargajiya, kamar irin su Fartanya da sauran makamantansu.”

Ministan ya kuma buga misali da shirin ciyar da ‘yan makaranta abinci, wanda ya yi nuni da cewa; idan har za a iya amfani da shirin wajen ciyar da ‘yan makarantar firamare miliyan 47, za a iya shayar da su da Madarar Shanu rabin Lita a kullum, za a iya samun bukatar litar ta Madarar a kasar, za ta karu zuwa sama da miliyan 23, a kullum, wanda hakan zai kuma kara taimakawa wajen samar da ayyukan yi a fannin na samar da Madarar, domin samun riba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

AI Zai Maye Gurbin Ayyuka Miliyan 92 A Duniya – Farfesa Pate

A ƙarshe, Farfesa Pate ya yabawa gwamnatin tarayya bisa gina sabbin gine-gine a jami’ar kamar ginin Majalisar Jami’a, katangar jami’a, da ɗakunan kwana. Ya bayyana cewa dalibai 6,870 ne suka kammala karatu, ciki har da 91 da suka samu First Class da kuma 16 da suka kammala karatun digiri na PhD. Haka kuma, jami’ar ta karrama mutane biyar da digirin girmamawa saboda gudummawarsu ga ci gaban kasa da ilimi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ASUU Ta Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Biya Albashin Watan Yuni
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Yace Mutanen Kasarsa Suna Cikin Shiri Don Kare Kansu Da Karfi
  • Gwamnatin Kasar Iran Ta Yi Allawadai Da Hare-Haren HKI Kan Kasar Yemen
  • Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki
  • Firaministan Kasar Sin: Kasarsa Ta Kimtsa Tsaf Wajen Inganta Aikin BRI Da Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Tare Da Habasha
  • Amurka za ta ɗauki nauyin ’yan tawaye domin yaƙi da ta’addanci
  • An Kaddamar Da Shirin Samar Da Wutar Lantarki A Jami’ar Kashere Gombe.
  • AI Zai Maye Gurbin Ayyuka Miliyan 92 A Duniya – Farfesa Pate
  • Gwamnatin Kasar Iran Ta Yaba Da Kungiyar BRICS Saboda Yin Tir Da HKI A Yakin Kwanaki 12
  • Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya