Ma’aikatar harkokin wajen Iran ta bayyana sabbin ci gaban da aka samu a tattaunawar da aka yi a birnin Roma

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Isma’il Baqa’i ya jaddada cewa: Ana gudanar da zagaye na biyar na tattaunawa ba na kai tsaye ba tsakanin tawagar Amurka da na Iran a cikin yanayi na kwarewa.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i ya bayyana a yau Juma’a cewa: Tattaunawar tana gudana cikin kwarewa da kwanciyar hankali, yana mai cewa abin da ake yadawa a kafafen yada labarai hasashe ne da baya da tushe ko inganci kuma baya da bambanci da shaci fadi.

A yau Juma’a da yamma ne aka fara shawarwarin da ba na kai tsaye ba karo na biyar tsakanin Iran da Amurka a hedkwatar wanzar da zaman lafiya ta masarautar Oman da ke birnin Roma fadar mulkin kasar Italiya.

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi da manzon Amurka na musamman Steve Witkoff ne ke jagorantar shawarwarin da masarautar Oman ke shiga tsakani.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: aikatar harkokin wajen harkokin wajen Iran

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Tana Da Karfi Wajen Tinkarar Hadari Da Kalubale A Fannoni Daban Daban

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning ta ce, a ranar 19 ga wannan wata, ofishin watsa labaru na majalisar gudanarwar kasar Sin ya yi bayani game da yanayin tafiyar tattalin arzikin kasar Sin a watan Afrilu, inda kafofin watsa labaru na kasa da kasa suka yi amfani da kalmomi kamar “wuce zaton da aka yi” da kuma “ da karfi” wajen yabawa tattalin arzikin kasar Sin.

Mao Ning ta bayyana hakan ne a gun taron manema labaru da aka gudanar a yau Laraba, inda ta ce, bisa yanayin tinkarar harajin kwastam mai yawa, kasar Sin ta tabbatar da bunkasar cinikayyar kasa da kasa.

A farkon watanni 4 na bana, yawan kudin kayayyakin shige da fice na kasar Sin ya karu da kashi 2.4 cikin dari, a cikinsu yawan kudin kayayyakin da aka fitar ya karu da kashi 7.5 cikin dari, lamarin da ya shaida cewa, Sin tana da karfin yin takara a duniya. Haka zalika, Sin ta kara bude kofa ga kasashen waje, da sa kaimi ga kamfanonin kasashen waje da su kara samun ci gaba da wuce zaton da aka yi a kasar. Wadannan duka sun shaida cewa, Sin tana da karfi wajen tinkarar hadari da kalubale a fannoni daban daban. (Zainab Zhang)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Ce: Amurka Ba Ta Fadan Hakikanin Abubuwan Da Aka Tattauna A Zamanta Iran 
  • INEC Ta Samar Da Sashen Ƙirƙirarriyar Basira Domin Inganta Harkokin Zaɓe 
  • Iran Ta Gamsu Da Lokaci Da Wurin Da Za A Gudanar Da Shawarwarinta Da Amurka Zagaye Na Biyar
  • Araghchi: Iran ba za ta tattauna kan batun inganta sinadarin Uranium din ta ba
  • Sin Tana Da Karfi Wajen Tinkarar Hadari Da Kalubale A Fannoni Daban Daban
  • Za’a Gudanar Da Tattaunawa Zagaye Na 5 Tsakanin Amurka Da Iran A Ranar 23-Afrilu A Roma
  • Sakataren Harkokin Wajen Amurka Ya Ce; Gwamnatin Siriya Zata Iya Rugujewa Cikin ‘Yan Makonni
  • Iran ba ta jiran izinin kowa kan tace uranium, Dole ne Amurka ta daina maganar banza_Jagora
  • EU ta dage takunkumin da ta kakaba wa Syria