Ma’aikatar harkokin wajen Iran ta bayyana sabbin ci gaban da aka samu a tattaunawar da aka yi a birnin Roma

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Isma’il Baqa’i ya jaddada cewa: Ana gudanar da zagaye na biyar na tattaunawa ba na kai tsaye ba tsakanin tawagar Amurka da na Iran a cikin yanayi na kwarewa.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i ya bayyana a yau Juma’a cewa: Tattaunawar tana gudana cikin kwarewa da kwanciyar hankali, yana mai cewa abin da ake yadawa a kafafen yada labarai hasashe ne da baya da tushe ko inganci kuma baya da bambanci da shaci fadi.

A yau Juma’a da yamma ne aka fara shawarwarin da ba na kai tsaye ba karo na biyar tsakanin Iran da Amurka a hedkwatar wanzar da zaman lafiya ta masarautar Oman da ke birnin Roma fadar mulkin kasar Italiya.

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi da manzon Amurka na musamman Steve Witkoff ne ke jagorantar shawarwarin da masarautar Oman ke shiga tsakani.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: aikatar harkokin wajen harkokin wajen Iran

এছাড়াও পড়ুন:

Sheikh Na’im Kasim Yace Kare Kasa Baya Bukatar Izini Daga Wani

Sheikh Na’in Kasem shugaban kungiyar Hizbullah ta kasar Lebanon ya bayyana cewa kungiyar bata bukatar Izini don kare kasar Lebanon daga makiyanta. Yama fadar haka ne ga wanda suka cika kunnen duniya kan cewa dole ne kungiyar ta mika makamanta ga gwamnatin kasar.

Kamfanin dillancin labaran Tasnim ya nakalto Sheikh Kasim yana fada a wani jawabin da ya gabatar a ranakun Ashoora na Imam Hussain (a) ta kafar Bidiyo. Ya kuma kara da cewa wadanda suke maganar kungiyar Hizbullah ta mika makamanta ga gwamnatinsa kasar, ya fiye masu sauki su fadawa yan mamaya su fice daga kasar Lebanon su kuma dakatar da hare-haren ta’addancin da suke kawo mata.

Ya kara jaddada cewa kungiyarsa zata ci gaba da rike makamanta sannan bata bukatar izini daga wani don kare-kasar Lebanon daga makiyanta.

Malaman ya kara da cewa, wani mai hankali ne zai amince ya mika makamansa a dai dai lokacinda mikiyan kasar Lebanon suna ci gaba da kawo hare-hare kan  kasar a ko wace rana. Maimakon su yi allawadai da mai shisgigi sai suka sa idanso a kan makaman hizbulla.

Yace idan wasu a kasar Lebanon sun zami mika kai ga HKI da Amurka to wannan zaminsa ne, amma mu ba masu mika kai ga makiyammu ne ba. Shi’arimmu shi ne {bama daukar kaskanci}.

Ya ce kun yi kuskure da kuka dogara da karfin wasu don takurawa masu gwagwarmaya. Masu gwagwarmaya basa jin tsoron makiya. Ya ce manufarmu ita ce yantar da kasa daga hannun makiya itace manufarmu.

Ya kammala da cewa makiyarmu it ace HKI, dole ne ta fice daga kasar Lebanon, kuma gwagwarmaya ita ce hanya tilo ta korar yan mamaya daga kasarmu. Idan kuma wani yana ganin akwai wata hanya korar makiya daga kasarmu a shirye muke mu shiga tataunawa da shi, ya gamsar damu a kan shirin nasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Firaministan Kasar Sin: Kasarsa Ta Kimtsa Tsaf Wajen Inganta Aikin BRI Da Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Tare Da Habasha
  • Araqchi Ya Gana Da Babban Malamin Yahudawa Mai Adawa Da ‘Yan Sahayoniyya A Gefen Taron Kungiyar BRICS
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Da Tawagarsa Sun Isa Kasar Brazil Don Halartar Taron BRICS Karo Na 17
  • Babban Mufti Na Masarautar Oman Ya Yi Kakkausar Suka Kan Masu Son Kulla Alaka Da H.K.Isra’ila
  • Iran ta Bukaci Gudanar da Bincike Kan Sacewar jami’ar Diblomasiyyar kasar A Lebanon Shekaru 43 Da Suka gabata
  •  IRGC: Duk Wani Wuce Gona Da Iri Na ‘Yan Sahayoniya Zai Gaggauta Rushewarsu
  • Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu
  • Al’ummar Iran Ba Zasu Amince Da Ci Gaba Da Zaman Tattaunawa Da Amurka Ba Saboda Fushin Da Suke Ciki Na Kai Musu Hari
  • Kasar Iran Ta Jaddada Wajabcin Hukunta Gwamnatin Mamayar Isra’ila Dangane Da  Ta’addancinta Kan Iran
  • Sheikh Na’im Kasim Yace Kare Kasa Baya Bukatar Izini Daga Wani