HausaTv:
2025-05-25@10:38:34 GMT

Rasha Ta Tarwatsa Makaman Ukiraniya A Tashar Jiragen Ruwa Ta Odessa

Published: 25th, May 2025 GMT

Kamfanin dillancin labarun Sputnik na Rasha ya sanar da cewa; sojojin kasar sun harba makamai masu linzami samfurin Iskander akan manyan akwatunan dakon kaya 100 dake dauke da makamai a tashar jiragen ruwa ta Odessa.

Sanarwar ta kuma kunshi cewa makaman da sojojin na Rasha su ka tarwatsa sun hada kananan jiragen ruwa na yaki na kai farmaki da ba su da matuki, jiragen sama marasa matuki, da kuma albarusai.

Haka nan kuma harin ya shafi manyan dakunan ajiye makamai a cikin tashar jiragen ruwan na Odessa.

Sanadiyyar wannan harin harshen wuta ya tashi wanda ya dauki lokaci yana ci.

 A gefe daya an yi musayar fursunoni a tsakanin sojojin Rasha da kuma na Ukiraniya wanda shi ne mafi girma tun da yaki ya barke a tsakanin kasashen biyu.

A wani gefen, har yanzu ana ci gaba da Magana akan tsagaita wutar yaki, da Amurka take son ganin ya faru, saboda kare manufofinta na dibar albarkun kasar ta Ukiraniya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran: Inda Makiya Kasar Sun San Cewa Zasu Sami Nasara A Kan Iran A Yaki Da Tuni Sunn Farmata Da Yaki

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa da Amurka da HKI sun san cewa zasu sami nasara a kan kasar Iran da yaki da tuni  sun fadawa kasar sun kuma mamayeta.

Amma saboda wannan tsoron ne suka zabi tattaunawa da ita a kan shirinta na makamshin nukliya. Sannan Shirin makamacin nikliya ma daya ne kacal daga matsalolin da ke tsakanin Iran da HKI da kuma kasashen yamma musamman Amurka.  Ya ce akwai matsaloli da dama, tana jirin ta kamala da gudu don ta bullo da wata. Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto ministan yana fadar haka a jiya da yamma ya kuma  kara da cewa, manufar Iran ta shiga tattaunawa da Amurka ita ce, samun ganin an daukewa kasar takunkuman tattalin arzikin da aka dora mata. Kuma ta zabi  hanyar diblomasiyya don samun hakan.

Arachi ya bayyana cewa kasashen yamma musamman Amurka sun dorawa kasar takunkuman tattalin arziki masu yawa, amma mafi  muhimmanci daga cikinsu su ne na makamashin nukliya, don Shirin makamashin nukliyar kasar ne Amurka ta dora mata takunkuman hana saida man fetur ta kuma rana bankunan kasar Iran da Swift, wato aikin da sauran bankunan a duniya. Kuma su ne suka fi cutar da tattalin arzikin kasar.  Daga karshe Aragchi ya bayyana cewa in akwai hanyar cira wadannan takunkuman Iran ba zata yi jiunkiri ba, amma kuma tana rayuwa da takunkuman tun shekar ta 2018. Amurka ta kasa cimma manufarta don wadannan takunkuman wanda kuma shine takurawa mutane su tashi su kifar da gwamnatin JMI wanda bai faru ba kuma ba zai faruba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran: Amurka Ta Shiga Tattaunawa Da Ita Ne Bayan Da Fahimci Daukar Matakin Soja Ba Zai Yi Amfani Ba
  • Yadda Za Ki Hada Garin Sakwara
  • ‘Yan Ta’adda Na Amfani Da Na’urorin Zamani Daidai Lokacin Da Sojoji Ke Da Karancin Makamai -Zulum
  • Iran: Inda Makiya Kasar Sun San Cewa Zasu Sami Nasara A Kan Iran A Yaki Da Tuni Sunn Farmata Da Yaki
  • Wani Dan Majalisar Dokokin Kasar Amurka Ya Bukaci Amurka Ta Jefa Makaman Nukliya Kan Gaza
  • Limamin Masallacin Jumma’a A Nan Tehran Ya Yi Magana Dangane Da Kwatar Garin Khurramshar Daga Sojojin Sadam
  • ‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Sun Kammala Aiki A Wajen Tashar Sararin Samaniyar Kasar Sin
  • Yawan Wutar Lantarkin Da Sin Ke Iya Samar Ta Amfani Da Karfin Ruwa Ta Kai Matsayin Koli A Duniya
  • Sojojin Yemen Sun Kai Wa Filin Jirgin Saman “Ben Gorion” Hari Sau Biyu A Yau Alhamis