Rasha Ta Tarwatsa Makaman Ukiraniya A Tashar Jiragen Ruwa Ta Odessa
Published: 25th, May 2025 GMT
Kamfanin dillancin labarun Sputnik na Rasha ya sanar da cewa; sojojin kasar sun harba makamai masu linzami samfurin Iskander akan manyan akwatunan dakon kaya 100 dake dauke da makamai a tashar jiragen ruwa ta Odessa.
Sanarwar ta kuma kunshi cewa makaman da sojojin na Rasha su ka tarwatsa sun hada kananan jiragen ruwa na yaki na kai farmaki da ba su da matuki, jiragen sama marasa matuki, da kuma albarusai.
Sanadiyyar wannan harin harshen wuta ya tashi wanda ya dauki lokaci yana ci.
A gefe daya an yi musayar fursunoni a tsakanin sojojin Rasha da kuma na Ukiraniya wanda shi ne mafi girma tun da yaki ya barke a tsakanin kasashen biyu.
A wani gefen, har yanzu ana ci gaba da Magana akan tsagaita wutar yaki, da Amurka take son ganin ya faru, saboda kare manufofinta na dibar albarkun kasar ta Ukiraniya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Rizai: Mun Harbo Jirage Kanana Da Manya 80 Na ‘Yan Sahayoniya
Tsohon kwamandan dakarun kare juyin juya halin musulunci na Iran Birgediya Muhsin Rizai, ya sanar da cewa; Dakarun IRGC sun yi nasarar harbo jirage manya da marasa matuki na HKI har guda 80, kuma da akwai baraguzai 32 daga cikinsu da ake rike da su.
Birgediya Rizai ya kuma kara da cewa; Daga cikin wadanda aka harbo din da akwai samfurin “Hermes” da “Hermon” da sune kira ta karshe da ‘yan sahayoniya suke takama da su.
Birgediya Muhsin Rizai wanda memba ne a majalisar fayyace maslahar tsarin musulinci ta Iran, wanda tashar talbijin ta yi hira da shi da marecen jiya Talata, ya yi Magana akan bangarori da dama na kallafaffen yakin kwanaki 12 inda ya ce:” Gabanin mu yi bitar yadda yakin ya kasance, ya zama wajibi mu yi Magana akan cewa, farfagandar da su ka yi, saboda matsin lambar da su ka rika fuskanta ne a cikin gida da kuma a Amurka sannan kuma a fagen duniya. Hakika ita ce Isra’ila ta ci kiasa a yakin. Matsin lambar ya kai ga cewa, Trump ya mayarwa da tashar talabijin irin CNN martani da cewa: Karya kuke yi, mun yi nasara.”
Musin Rizai ya kuma ce; Idan mu ka duba akan ko sun yi nasara, ko a’a, za mu yi nazari akan asarar kudade bisa abinda ma’aikatar kudi ta HKI ta fitar. Sun bayyana cewa, sun yi asarar kudaden da sun kai dalar Amurka biliyan 20 a cikin kwanaki 12 kadai. Kuma Na’urorin kakkabo makamai masu linzami samfurin Thaad da aka kera a cikin shekaru biyu,sun kare. A cikin kwanaki 12, sun karar da na’urorin da su ka dauki shekaru biyu suna kerawa.”
Birgediya Rizai ya kuma bayyana yadda na’urorin Rada na Iran su ka dauko hotunan jikkata da kakkabo jiragen abokan gaba 80 daga cikinsu da akwai baraguzai 32 da ake rike da su.”