Arakci Ya Jaddada Muhimmanci Kawo Karshen Yakin Gaza Da Kuma Shigar Da Kayan Agaji
Published: 24th, May 2025 GMT
Ministan harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran, Abbas Arakci wanda ya gana da takwransa na fadar Vatican ya yi kira da a kawo karshen laifukan da ‘yan mamaya suke tafkawa akan Gaza da gaggawa a kuma shigar da kayan agaji zuwa yankin.
Ministan harkokin wajen na Iran wanda ya je kasar Italiya domin tattaunawar bayan fage da Amurka akan Shirin kasarsa na Nukiliya, ya ziyarci fadar Vatican, inda ya gana da ministanta na harkokin wajen Cardinal paul Gallagher, ya mika sakon ta’aziyyar rasuwar Fafaroma Farancis sannan kuma da murnar zabar sabon Fafaroma Leo na 14
Abbas Arakci ya yi wa shugabannin fadar ta Vatican bayani akan matsayar Jamhuriyar musulunci ta Iran dangane da shirinta na Nukiliya na zaman lafiya, da kuma inda aka kwana a tattaunawar bayan fage da Amurka.
Haka nan kuma ya yi bayani akan matsayar Iran akan kisan kiyashin da ake yi wa al’ummar Gaza, tare da yin kira da a kawo karshensa da kuma shigar da kayan agaji zuwa yankin.
Haka nan kuma ya yi bayani akan yadda Iran take ganin za a iya warware matsalar mamaya a Falasdinu da ita ce yin kuri’ar raba gardaga da dukkanin Falasdinawa,musulmi kiristoci da yahudawa za su shiga a ckin tsarin demokradiyya.
A karshe bangarorin biyu sun jaddada muhimmanci tattaunawa a tsakanin addinai domin shimfida sulhu da zaman lafiya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Kasar Iran Ta Yaba Da Kungiyar BRICS Saboda Yin Tir Da HKI A Yakin Kwanaki 12
Ministan harkokin wajen kasar Iran wanda yake halattan taron kungiyar raya tattalin arziki ta Bricks ya yabawa kungiyar kan yin tir da Amurka da kuma HKI kan keta hurumin kasar da yaki na kwanaki 12 da kuma da kuma kaiwa cibiyoyin nukliyar kasar ta zaman lafiya wadanda suke Fordo Natanz ta kuma Esfahan.
Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ya nakalti ministan yana fadar haka a taron kungiyar karo 17 wanda ke gudana a hilin yanzu a birnin Rio De jenero na kasar Brazil.
A ranar 13 ga watan Yunin da ya gabata ne jiragen yaki na HKI suka kutsa cikin Iran inda suka kashe manya-manyan kwamandocin sojojin kasar da kuma masana fasahar Nukliyar kasar ga shahada.
Bayan haka sojojin yahudawan sun kai hare-hare kan tashar talabijin ta “Khabar” na harshen farisanci a hukumar tashoshin radio da talabijin na kasar.
Banda haka jiragen yakin Amurka B-2 sun kai hare0hare kan cibiyoyin Nukliyar kasar guda ukku.