Ministan harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran, Abbas Arakci  wanda ya gana da takwransa na fadar Vatican ya yi kira da a kawo karshen  laifukan  da ‘yan mamaya suke tafkawa akan Gaza da gaggawa a kuma shigar da kayan agaji zuwa yankin.

Ministan harkokin wajen na Iran wanda ya je kasar Italiya domin tattaunawar bayan fage da Amurka akan Shirin kasarsa na Nukiliya, ya ziyarci fadar Vatican, inda ya gana da ministanta na harkokin wajen Cardinal paul Gallagher, ya mika sakon ta’aziyyar rasuwar Fafaroma Farancis sannan kuma da murnar zabar sabon Fafaroma Leo na 14

Abbas Arakci ya yi wa shugabannin fadar ta Vatican bayani akan matsayar Jamhuriyar musulunci ta Iran dangane da shirinta na Nukiliya na zaman lafiya, da kuma inda aka kwana a tattaunawar bayan fage da Amurka.

Haka nan kuma ya yi bayani akan matsayar Iran akan kisan kiyashin da ake yi wa al’ummar Gaza, tare da yin kira da a kawo karshensa da kuma shigar da kayan agaji zuwa yankin.

Haka nan kuma ya yi bayani akan yadda Iran take ganin za a iya warware matsalar mamaya a Falasdinu da ita ce yin kuri’ar raba gardaga da dukkanin Falasdinawa,musulmi kiristoci da yahudawa za su shiga  a ckin tsarin demokradiyya.

A karshe bangarorin biyu sun jaddada muhimmanci tattaunawa a tsakanin addinai domin shimfida sulhu da zaman lafiya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Yakin Gaza : Tarayyar Turai za ta sake nazari kan Yarjejeniyarta da Isra’ila

Bayan sabon farmakin da Isra’ila ta kai a zirin Gaza, kasashen Yamma na kokarin kara matsin lamba kan Isra’ila, wacce ta kauda kai kan kiraye kirayen da duniya ke yi na ta dakatar da yakin a Gaza.

Kungiyar ta EU, ta kara mastin lamba ta hanyar sake nazari kan yarjejeniyarta da Isra’ila ta tsawon shekaru 25 dake a tsakaninsu.

Tunda farko dama kasashen kasashen Canada-Faransa da Ingila  sun sanar da yin Allah wadai da farmakin kasa na soja na sojojin Isra’ila a Gaza.

Baya ga hakan kuma Birtaniyya a ranar Talata ta sanar da kawo karshen yarjejeniyar ciniki cikin ‘yanci da Isra’ila.

Ita ma kiasar Sweden, ta yi kira da a kakaba takunkumi ga membobin gwamnatin Isra’ila.

Bayanai sun ce yanzu haka matakan da wasu kasashen yamma ke doka , ya hadassa sabani tsakanin kasashe 27 na Tarayyar Turai.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Guterres: MDD Ba Za Ta Shiga Duk Wani Shiri Da Ba Zai Girmama Dokokin Kasa Da Kasa Ba A Gaza
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Kara Haske kan Batun Inganta Sinadarin Uranium Da Zamanta Da Amurka
  • Iran Ta Ce: Amurka Ba Ta Fadan Hakikanin Abubuwan Da Aka Tattauna A Zamanta Iran 
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Ce; Ba Ta Gaggawar Neman Kulla Alaka Da Kasar Siriya
  • Yakin Gaza : Tarayyar Turai za ta sake nazari kan Yarjejeniyarta da Isra’ila
  • Madagascar ta kawo karshen cutar shan inna a tsibirin
  • Wasu Yahudawa Sun Hana Kayakin Agaji Shiga Yankin Gaza
  • Sakataren Harkokin Wajen Amurka Ya Ce; Gwamnatin Siriya Zata Iya Rugujewa Cikin ‘Yan Makonni
  • Babban Muftin Oman Ya Yi Suka Kan Taron Kungiyar Larabawa Saboda Rashin Saboda Rashin Ba Wa Gaza Muhimmanci