Aminiya:
2025-05-24@18:05:23 GMT

An fara aikin gina mayankar dabbobi ta Naira biliyan 3 a Gombe

Published: 24th, May 2025 GMT

Gwamnatin Jihar Gombe ta sanya hannu kan yarjejeniyar Naira biliyan uku domin gina mayankar dabbobi ta zamani a garin Gombe.

Hakan wani bangare ne na shirin inganta kiwon dabbobi da tsaftar abinci da kuma rage matsalolin kiwon dabbobi (L-PRES) wanda Bankin Duniya ke tallafa wa. Shirin L-PRES na da nufin kyautata harkar kiwon dabbobi da sarrafa nama cikin tsafta a jihar.

An kulla yarjejeniyar ce tare da kamfanin Lubel Nigeria Limited da wa’adin kammalawa na watanni 9, zuwa watan Fabrairun shekarar 2025.

An gudanar da bikin sanya hannu kan yarjejeniyar a ofishin L-PRES da ke G.R.A, a Gombe, inda shugaban shirin na jihar, Farfesa Usman Bello Abubakar, ya bayyana wannan aiki a matsayin babban ci-gaba a jihar.

Sojoji sun kashe mayaƙan ISWAP 5 a Borno Yadda dilolin ƙwaya ke cin karensu ba babbaka a Abuja

“Wannan ba kawai wurin yanka dabbobi ba ne, amma zuba jari ne ga ci-gaban kiwon dabbobinmu. Za mu tabbatar da aiki da ka’idojin duniya wajen tsafta, yanka, da sarrafa nama,” in ji shi.

Farfesa Abubakar ya kuma yaba wa Gwamna Inuwa Yahaya saboda hangen nesansa wajen kyautata kayan more rayuwa da bunkasa tattalin arzikin jihar.

Shugaban gudanarwa na kamfanin Lubel Nigeria Limited, Akitet Yunusa Yakubu, ya yi alkawarin kammala aikin cikin inganci da kuma a kan lokaci, tare da alkawarin cika dukkan sharudda domin tabbatar da nasarar aikin.

Da zarar an kammala wannan mayankar dabbobi na zamani, ana sa ran zai kawo sauyi mai amfani ga harkar sarrafa nama a Jihar Gombe, da rage hadarin rashin tsafta da ke tattare da hanyoyin gargajiya, tare da samar da damammaki a cikin darajar kiwon dabbobi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: mayanka

এছাড়াও পড়ুন:

An kama wani matashi da ya yi shigar mata a Adamawa

Rundunar ’yan sandan Jihar Adamawa ta kama wani mai suna Mohammed Umar mai shekara 19, mazaunin wata unguwa da ake kira hanyar Abuja a ƙaramar hukumar Yola ta Kudu bisa laifin sanya tufafi da shigar mata.

Kakakin rundunar ’yan sandan, SP Suleiman Ngoruje, a wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba ya bayyana cewa, mutumin yana ta kai-kawo a cikin harabar cocin Ngurore Lutheran Church of Christ Nigeria.

Dangote ya sake rage farashin man fetur An yi Jana’izar Shugaban Ƙungiyar Masu Shirya Finafinai ta Ƙasa a Zariya

“Kamen matashi ya biyo bayan rahoton da wani mazaunin garin (da aka sakaya sunansa) ya kai hedikwatar ’yan sanda ta Ngurore, bayan ya lura da sintirin wanda ake zargin a cikin harabar cocin.”

A cewar sanarwar, Kwamishinan ’yan sandan Jihar Adamawa, Dankombo Morris, ya bayar da umarnin a mayar da batun zuwa sashin binciken manyan laifuka na Jihar, da ke Yola, domin gudanar da sahihin bincike.

“Rundunar ta ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da tsaron jama’a, da zaman lafiyar jama’a da kuma ƙarfafa wa mazauna yankin gwiwa da su sanya ido tare da bayar da rahotannin wasu da ake yi zargi ga ‘yan sanda kan lokaci,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hakar man Kolmani: Jihohin Bauchi da Gombe sun gana da NNPC kan bukatun al’umma
  • Nijeriya Na Da Karfin Tattalin Arzikin Sarrafa Kayan Dandanon Da Muke Bukata A Cikin Gida – Yahaya Yakubu
  • Mace ta damfari masu neman aikin gwamnati Naira miliyan 250
  • Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (2)
  • An kama wani matashi da ya yi shigar mata a Adamawa
  • Rukunin Karshe Na Alhazan Jigawa Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
  • Jirgin Karshe Na Alhazan Jihar Kwara Ya Isa Kasa Mai Tsarki
  • Kotu Ta Soke Umarnin Kwace Filin Asibitin Tiamin, Ta Umarci Gwamnatin Kano Ta Biya Diyyar Biliyan ₦2.6bn