Aminiya:
2025-09-17@21:53:57 GMT

An fara aikin gina mayankar dabbobi ta Naira biliyan 3 a Gombe

Published: 24th, May 2025 GMT

Gwamnatin Jihar Gombe ta sanya hannu kan yarjejeniyar Naira biliyan uku domin gina mayankar dabbobi ta zamani a garin Gombe.

Hakan wani bangare ne na shirin inganta kiwon dabbobi da tsaftar abinci da kuma rage matsalolin kiwon dabbobi (L-PRES) wanda Bankin Duniya ke tallafa wa. Shirin L-PRES na da nufin kyautata harkar kiwon dabbobi da sarrafa nama cikin tsafta a jihar.

An kulla yarjejeniyar ce tare da kamfanin Lubel Nigeria Limited da wa’adin kammalawa na watanni 9, zuwa watan Fabrairun shekarar 2025.

An gudanar da bikin sanya hannu kan yarjejeniyar a ofishin L-PRES da ke G.R.A, a Gombe, inda shugaban shirin na jihar, Farfesa Usman Bello Abubakar, ya bayyana wannan aiki a matsayin babban ci-gaba a jihar.

Sojoji sun kashe mayaƙan ISWAP 5 a Borno Yadda dilolin ƙwaya ke cin karensu ba babbaka a Abuja

“Wannan ba kawai wurin yanka dabbobi ba ne, amma zuba jari ne ga ci-gaban kiwon dabbobinmu. Za mu tabbatar da aiki da ka’idojin duniya wajen tsafta, yanka, da sarrafa nama,” in ji shi.

Farfesa Abubakar ya kuma yaba wa Gwamna Inuwa Yahaya saboda hangen nesansa wajen kyautata kayan more rayuwa da bunkasa tattalin arzikin jihar.

Shugaban gudanarwa na kamfanin Lubel Nigeria Limited, Akitet Yunusa Yakubu, ya yi alkawarin kammala aikin cikin inganci da kuma a kan lokaci, tare da alkawarin cika dukkan sharudda domin tabbatar da nasarar aikin.

Da zarar an kammala wannan mayankar dabbobi na zamani, ana sa ran zai kawo sauyi mai amfani ga harkar sarrafa nama a Jihar Gombe, da rage hadarin rashin tsafta da ke tattare da hanyoyin gargajiya, tare da samar da damammaki a cikin darajar kiwon dabbobi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: mayanka

এছাড়াও পড়ুন:

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

An garzaya da ita asibiti, amma daga baya likitoci suka tabbatar da mutuwarta.

’Yansanda sun kama Bosede kuma suna bincike a kan lamarin.

Kakakin rundunar, DSP Olusola Ayanlade, ya ce za su tabbatar da adalci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba
  • Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka
  • An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a Gombe
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
  • Kukan al’umma kan lalacewar hanyar Dukku
  • Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo
  • NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
  • Ɗangote zai gina ɗakunan kwanan ɗalibai 250  a Jami’ar Ilorin