Aminiya:
2025-06-10@00:01:34 GMT

Halin da fasinjoji ke ciki bayan hatsarin jirgin sama a Ilori

Published: 24th, May 2025 GMT

Hukumar Binciken Tsaro ta Najeriya (NSIB) ta sanar cewa mutanen da suka tsallake rijiya da baya a hatsarin jirgin sama da ya auku a Jihar Kwara suna samun kulawa a asibiti

Da yake tabbatar da cewe duka mutanen cikin jirgin horon sun tsira da ransu, Babban Daraktan NSIB, Kyaftin Alex Badeh Junior, ya ce hukumar ta gano katin nadar bayanai daga jirgin, bayan aukuwar hatsarin a filin jirgin sama na Janar Tunde Idiagbon da ke Ilorin,

Jirgin, nau’in Diamond, mai lamba BNI, mallakin Kwalejin Koyon Tukin Jiragen Sama ta Ilorin (IAC) ne, kuma ya yi hatsarin ne a yayin atisayen sauka na gwaji, inda ya kauce daga titi, ya yi cikin daji ya lalace fiye da yadda za a iya gyarawa.

Kyaftin Badeh ya bayyana Ya ce wadanda ya yi hatsari da su sun hada da shugaban horo, wanda aka sani da Ajape, da wata daliba, Lola. Dayansu ya samu rauni mai tsanani, ɗayan kuma ya samu raunuka marasa yawa, kuma dukansu suna karbar magani a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Ilorin (UITH).

Hakar man Kolmani: Jihohin Bauchi da Gombe sun gana da NNPC kan bukatun al’umma Za mu gina mayankar dabbobi a kan Naira biliyan 3 a Gombe —Gwamnati

Ya bayyana cewa ana nazarin katin bayanan da aka gano a dakin gwaje-gwajen NSIB, kuma ana sa ran za a fitar da rahoton farko cikin kwanaki 30 masu zuwa.

Ya jaddada cewa aikin hukumar shi ne gano abin da ya faru da kuma yadda za a hana sake faruwar irinsa a nan gaba, yana mai tabbatar wa jama’a cewa duk da hatsarin da ya faru, sararin samaniyar Najeriya yana nan cikin aminci.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hatsarin jirgi

এছাড়াও পড়ুন:

Ghana Ta Kawo Karshen Goyon Bayan Da Take Bawa Kungiyar Polisario

Kasar Ghana ta kawo karshen goyon bayan da take bawa kungiyar Polisario, sannan ta dawo tana goyon bayan kasar Morocco a kan wannan rikicin.

Shafin yanar gizo na labarai Africa News ya bayyana cewa, an kafa kungiyar Polisario ne a shekara 1979. Sannan rikicin Polisario yana komawa zuwa shekara 1975 a lokacinda turawan Espania yan mulkin mallaka suka fice daga yankin sai suka hadda fada tsakanin Polisario da kasashen Morocco da kuma Mauritania.

Kungiyar dai tana samun goyon bayan kasashe kimani 80 a duniya, amma kuma a hankali-a hankali tana rasa goyon bayan da take da samu a duniya, na karshensu it ace kasar Ghana.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila ta ƙwace jirgin ruwa a hanyar kai agaji Gaza
  • Hatsarin Mota Ya Yi Ajalin Mutane 9 A Jigawa
  • HKI Ta Kaiwa Jirgin Ruwan Masu Rajin Kare Hakkin Mutanen Gaza Na Jinkai Wato Madleen
  • HKI Ta Kaiwa Jirgin Ruwan Masu Rajin Kare Hakkin Mutanen Gaza Na Jinkai
  • Mutum 9 sun rasu a hatsarin mota a Jigawa
  • Jirgin Ruwa “Madeleine” Dake Son Karya Takunkumin Gaza Yana Ci Gaba Da Tafiya
  • Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki
  • Ghana Ta Kawo Karshen Goyon Bayan Da Take Bawa Kungiyar Polisario
  • Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
  • Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne