Aminiya:
2025-06-12@00:54:05 GMT

Halin da fasinjoji ke ciki bayan hatsarin jirgin sama a Ilori

Published: 24th, May 2025 GMT

Hukumar Binciken Tsaro ta Najeriya (NSIB) ta sanar cewa mutanen da suka tsallake rijiya da baya a hatsarin jirgin sama da ya auku a Jihar Kwara suna samun kulawa a asibiti

Da yake tabbatar da cewe duka mutanen cikin jirgin horon sun tsira da ransu, Babban Daraktan NSIB, Kyaftin Alex Badeh Junior, ya ce hukumar ta gano katin nadar bayanai daga jirgin, bayan aukuwar hatsarin a filin jirgin sama na Janar Tunde Idiagbon da ke Ilorin,

Jirgin, nau’in Diamond, mai lamba BNI, mallakin Kwalejin Koyon Tukin Jiragen Sama ta Ilorin (IAC) ne, kuma ya yi hatsarin ne a yayin atisayen sauka na gwaji, inda ya kauce daga titi, ya yi cikin daji ya lalace fiye da yadda za a iya gyarawa.

Kyaftin Badeh ya bayyana Ya ce wadanda ya yi hatsari da su sun hada da shugaban horo, wanda aka sani da Ajape, da wata daliba, Lola. Dayansu ya samu rauni mai tsanani, ɗayan kuma ya samu raunuka marasa yawa, kuma dukansu suna karbar magani a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Ilorin (UITH).

Hakar man Kolmani: Jihohin Bauchi da Gombe sun gana da NNPC kan bukatun al’umma Za mu gina mayankar dabbobi a kan Naira biliyan 3 a Gombe —Gwamnati

Ya bayyana cewa ana nazarin katin bayanan da aka gano a dakin gwaje-gwajen NSIB, kuma ana sa ran za a fitar da rahoton farko cikin kwanaki 30 masu zuwa.

Ya jaddada cewa aikin hukumar shi ne gano abin da ya faru da kuma yadda za a hana sake faruwar irinsa a nan gaba, yana mai tabbatar wa jama’a cewa duk da hatsarin da ya faru, sararin samaniyar Najeriya yana nan cikin aminci.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hatsarin jirgi

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Leken Asiri Na Iran Ya Yi Karin Bayani Kan Nasarar Samun Bayan Tsaron HKI

Ministan leken asiri na kasar Iran ya ce asiran tsaron HKI da suka shiga hannun ma’aikatansa sun shafi makaman nukliya na HKI kuma sun nuna kwarewar da jami’an leken asirin kasar suke da shi.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa wannan bayanan zasu taimakawa sojojin JMI wajen sanin wuraren da zasu kai hare hare a duk lokacinda yake ya barke tsakanin Iran da haramtacciyar kasar, na makamai da kuma na yanar gizo.

Labarin ya kara da cewa  da jami’an ma’aikatar hukumar leken asiri suka yi kama daga daukar ma’aikatan da suka dace da yin hakan da dabar barun da suke yi amfani da su don kaiwa da bayan da suke bukata ya nuna irin koreawarsu a wannan aikin.

Sannan daga cikin muhimman bayanan da suka samu sun hada da na makaman nukliyar haramtacciyar kasar da kuma dangantakanta da Amurka da kuma kasashen turai rawar da wadan nan kasashe suka taka a karfafa HKI kan makamanta na kissan kaere dangi.

Ministan ya kammala da cewa bayanan da muka samu suna da muhimmanci haka ma hanyar da muka bi muka kai ga bayanan suna da muhimmanci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jagora Ya Bambance Tsakanin Majalisun Dokokin Kasashe A Fagen Gudanar Da Ayyukan Kasa
  • Gwamnatin Kano za ta binciki musabbabin gobarar kasuwar Farm Center
  • Nan Ba Da Jimawa Ba Harkar Man Fetur Za Ta Sauya A Nijeriya – Dangote
  • Sojojin Yemen Sun Kai Farmakin Kan Tashar Jiragen Sama Na Bengerion A HKI
  • WHO : har yanzu kyandar biri na da matukar hadari ga duniya
  • Isra’ila ta ƙwace jirgin ruwa a hanyar kai agaji Gaza
  • Hatsarin Mota Ya Yi Ajalin Mutane 9 A Jigawa
  • HKI Ta Kaiwa Jirgin Ruwan Masu Rajin Kare Hakkin Mutanen Gaza Na Jinkai Wato Madleen
  • Ministan Leken Asiri Na Iran Ya Yi Karin Bayani Kan Nasarar Samun Bayan Tsaron HKI
  • HKI Ta Kaiwa Jirgin Ruwan Masu Rajin Kare Hakkin Mutanen Gaza Na Jinkai