Aminiya:
2025-11-03@12:34:20 GMT

Jami’an Sibil Difens sun bude wuta a garin Jos

Published: 24th, May 2025 GMT

Mazauna garin Jos sun shiga cikin zullumi bayan da jami’an Hukumar Tsaro ta Sibil Difens (NSCDC) suka yi ta harbe-harbe a ranar Asabar.

Jami’an na Sibil Difens da ke aiki karkashi Hukumar Kula da Ci-gaban Garin Jos (JMDB) sun bude wuta ne a yayin wani samame da suka kai katafare shagon sayar da kayayyaki na S.

O Plaza, lamarin da ya haifar da rikici.

Jami’an hukumar sun kuma lakada wa wani matashi mai aiki a plazar duka, lamarin da ya rincabe zuwa tayar da jijiyoyin wuya.

A yayin samamen, jami’an tsaron sun ce sun je ne domin kama wata babbar mota da ta keta dokar  hana manyan motoci shiga garin.

Za mu gina mayankar dabbobi ta Naira biliyan 3 a Gombe —Gwamnati Sojoji sun kashe mayaƙan ISWAP 5 a Borno

Amma wani bidiyo da ke yawo ya nuna cewa an ajiye motar ce a cikin harabar plazar kuma ba ta tare hanya ba.

Mazauna garin Jos sun bayyana cewa ba jami’an da ke aiki da JMDB sun yi kaurin suna wajen yin irin haka, inda suke lalata dukiyar jama’a a yayin samamen da suk kaiwa tare da nuna karfin makamai, da ke jefa jama’a cikin firgici.

Mamallakin S.O Plaza, Mista Solomon Okeke, the owner of S.O Plaza, ya bayyana abin a matsayin barna.

Ya kara da cewa ko a watan Agustan bara, wani Manajan Hukumar JMDB, Hart Bankat, ya jagoranci jami’an Sibil Difens zuwa plazar ya sa suka harbe tayoyi shida na wata babbar mota a cikin harabar wurin, wanda ya jawo musu asarar miliyoyin kudade.

Mista Okeke ya bayyana cewa jami’an “sun yi awon gaba da wata babbar mota cike da kaya, kuma sun yi wa wani dan shekara 19 duka suka yayyaga masa kaya, kuma har yanzu ba a san inda yak ba.

“Me ya sa duk lokacin da suka zo sai sun yi ta harbe-harbe suna dukan ma’aikata sun lalata dukiyar jama’a?”

A nasu bangaren, mazauna yakin na Bukuru sun bukaci Gwamna Caleb Mutfwang ya sanya baki tare da taka wa jami’an JMDB burki kan irin yadda suke wuce gona da iri domin a samu zaman lafiya.

Wakilinmu ya yi kokarin jin ta bakin Janar Manajan JMDB, Akitet Hart Bankat, amma har zuwa lokacin da aka kammala wannan rahoton haka bai samu ba, saboda jami’in bai ba da amsa ga tambayar da aka yi masa ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Harbe harbe

এছাড়াও পড়ুন:

Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar October 31, 2025 Manyan Labarai NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa October 31, 2025 Labarai Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila ta aikata laifuka 194 tun bayan tsagaita wuta a Gaza
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • ‘An Kashe Masu Zanga-zanga Akalla 500 a Tanzania’
  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • An yi garkuwa da Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Kebbi
  • HKI Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza Inda Take Kashe Falasdinawa
  • Kasashen Pakistan Da Afghanistan Sun Tsawaita Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta
  • Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa
  • An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m