Jami’an Sibil Difens sun bude wuta a garin Jos
Published: 24th, May 2025 GMT
Mazauna garin Jos sun shiga cikin zullumi bayan da jami’an Hukumar Tsaro ta Sibil Difens (NSCDC) suka yi ta harbe-harbe a ranar Asabar.
Jami’an na Sibil Difens da ke aiki karkashi Hukumar Kula da Ci-gaban Garin Jos (JMDB) sun bude wuta ne a yayin wani samame da suka kai katafare shagon sayar da kayayyaki na S.
Jami’an hukumar sun kuma lakada wa wani matashi mai aiki a plazar duka, lamarin da ya rincabe zuwa tayar da jijiyoyin wuya.
A yayin samamen, jami’an tsaron sun ce sun je ne domin kama wata babbar mota da ta keta dokar hana manyan motoci shiga garin.
Za mu gina mayankar dabbobi ta Naira biliyan 3 a Gombe —Gwamnati Sojoji sun kashe mayaƙan ISWAP 5 a BornoAmma wani bidiyo da ke yawo ya nuna cewa an ajiye motar ce a cikin harabar plazar kuma ba ta tare hanya ba.
Mazauna garin Jos sun bayyana cewa ba jami’an da ke aiki da JMDB sun yi kaurin suna wajen yin irin haka, inda suke lalata dukiyar jama’a a yayin samamen da suk kaiwa tare da nuna karfin makamai, da ke jefa jama’a cikin firgici.
Mamallakin S.O Plaza, Mista Solomon Okeke, the owner of S.O Plaza, ya bayyana abin a matsayin barna.
Ya kara da cewa ko a watan Agustan bara, wani Manajan Hukumar JMDB, Hart Bankat, ya jagoranci jami’an Sibil Difens zuwa plazar ya sa suka harbe tayoyi shida na wata babbar mota a cikin harabar wurin, wanda ya jawo musu asarar miliyoyin kudade.
Mista Okeke ya bayyana cewa jami’an “sun yi awon gaba da wata babbar mota cike da kaya, kuma sun yi wa wani dan shekara 19 duka suka yayyaga masa kaya, kuma har yanzu ba a san inda yak ba.
“Me ya sa duk lokacin da suka zo sai sun yi ta harbe-harbe suna dukan ma’aikata sun lalata dukiyar jama’a?”
A nasu bangaren, mazauna yakin na Bukuru sun bukaci Gwamna Caleb Mutfwang ya sanya baki tare da taka wa jami’an JMDB burki kan irin yadda suke wuce gona da iri domin a samu zaman lafiya.
Wakilinmu ya yi kokarin jin ta bakin Janar Manajan JMDB, Akitet Hart Bankat, amma har zuwa lokacin da aka kammala wannan rahoton haka bai samu ba, saboda jami’in bai ba da amsa ga tambayar da aka yi masa ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Harbe harbe
এছাড়াও পড়ুন:
A Bai Wa Kudu Tikitin Takara A 2027 Ko PDP Ta Ruguje – Wani Jigo A PDP
Ya ƙara da cewa babu wani ɗan siyasa da zai iya lashe zaɓe shi kaɗai.
“Ku bai wa Kudu tikitin, ku ga sakamako. Amma idan PDP ta ci gaba da tafiya a kan wannan kuskure, to, za ta fuskanci babbar matsala a 2027,” Yusuf ya bayyana.
Ya kuma bayyana cewa Atiku Abubakar ba ɗa jam’iyyar PDP ba ne a yanzu, yana tare da wata sabuwar tafiyar haɗin gwiwa ta siyasa.
Yusuf ya ɗora alhakin faɗuwar jam’iyyar a zaɓen 2023 kan rashin kyakkyawan shugabanci da kuma rabon tikiti ba bisa ƙa’ida ba.
Ya ce rikicin cikin gida da kuma gazawar PDP wajen kulawa da ‘yan Kudu ne suka sa jam’iyyar ta faɗi.
Ya kuma nuna takaicinsa game da sauya sheƙar Gwamnan Jihar Delta na baya, Ifeanyi Okowa, zuwa jam’iyyar APC, yana mai cewa hakan na nuna cewa PDP ta kasa tsara kamfen ɗinta yadda ya dace.
Ya buƙaci shugabannin PDP da su daina dogaro da tsofaffi a siyasa, su mayar da hankali wajen gina sabuwar amana da haɗin kai, musamman a yankin Kudu.
A cewarsa, adalci, haɗin gwiwa, da sake gina jam’iyya su ne kawai hanyar da PDP za ta iya dawowa da ƙarfi a zaɓen 2027.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp