UNICEF ta gabatar da asusun abinci na yara don karfafa zuba jari a cikin manufofi da shirye-shirye. UNICEF ta jajirce wajen yin hadin gwiwa da gwamnatin Jihar Kwara don yaki da rashin abinci mai gina jiki, musamman a lokacin kwana 1000 na farko na rayuwar yara.

“Kalubalen shi ne, yawan yara fiye da kashi 40 cikin 100 suna da gwannan matsala kuma kusan yara 300,000 suna fuskantar samun kulawar gaggawa don magance wadannan matsaloli.

Ta danganta dalilan rashin abinci mai gina jiki ga sakamakon talauci, canjin yanayi, rashin samun abinci, da kuma matsalolin tsaro.

A nasa jawabin, Gwamna Jihar Kwara, AbdulRaman AbdulRazak, wanda ya samu wakilcin Sakataren gwamnatin jihar, Farfesa Jubril Shaaba Mamman, ya bayyana cewa, tasiri mai kyau game da rayuwar yara na Jihar Kwara shi ne, samun abinci mai gina jiki, wanda wannan ya sa aka yanke shawarar karbar shirin asusun samar da abinci mai gina jiki ga yara na UNICEF.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Yara

এছাড়াও পড়ুন:

MDD ta yi gargadin cewa jarirai 14,000 a Gaza kan iya mutuwa idan an ci gaba da killace Zirin 

Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadin cewa jarirai dubu 14 a Gaza kan iya rasa rayukansu muddin Irsa’ila ta ci gaba da killace Zirin da hana shigar da kayan agaji.

Mataimakin Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Tom Fletcher na maida martini ne kan matakin gwmanatin Isra’ila na kyale manyan motoci hudu na agaji su shiga Gaza inda ya ce wannan tamkar”digo ne a cikin teku.”

“Akwai jarirai 14,000 da za su mutu a cikin sa’o’i masu zuwa idan ba za mu iya kaiwa gare su ba inji shi.

Ya ce motocin agajin da ke dauke da kayan abinci na jarirai da abinci mai gina jiki, suna cikin Gaza amma ba su kai ga farar hula ba saboda gwamnatin Isra’ila ba ta yarda da hakan ba.

Halin jin kai a Gaza ya ta’azzara sosai tun daga ranar 18 ga Maris saboda yadda gwamnatin Isra’ila ta takaita shigar abinci, man fetur, magunguna, da ruwa cikin Zirin na Gaza.

A cewar hukumar Integrated Food Security Phase Classification (IPC), kusan yara 71,000 ‘yan kasa da shekaru biyar suna fuskantar barazanar rashin abinci mai gina jiki.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rashin abinci mai gina jiki a Gaza ya yi sanadiyar mutuwar mutane 299
  • An fara aikin gina mayankar dabbobi ta Naira biliyan 3 a Gombe
  • Gyaran Jiki Da Kyawun Fata
  • Nijeriya Na Da Karfin Tattalin Arzikin Sarrafa Kayan Dandanon Da Muke Bukata A Cikin Gida – Yahaya Yakubu
  • Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Yadda Tabarbarewar Tsaro Ta Kara Yawan Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta
  • Gwamnatin Tarayya Ta Kashe Naira Tiriliyan 1.5 Don Magance Matsalar Abinci — Minista
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Nasarorin Noma da Tsaron Abinci Karkashin Shirin Renewed Hope
  • MDD ta yi gargadin cewa jarirai 14,000 a Gaza kan iya mutuwa idan an ci gaba da killace Zirin