Sojoji sun kashe mayaƙan ISWAP 16 a Bormo
Published: 23rd, May 2025 GMT
Dakarun sojojin Najeriya na Operation Haɗin Kai da rundunar sojin sama sun daƙile wani harin haɗin gwiwa da ‘yan ta’addar ISWAP suka kai a garin Damboa, inda suka kashe mahara 16 a wani ƙazamin faɗa da suka yi cikin dare.
Mai sharhi kan lamarin tsaro Zagazola Makama ya samu labarin cewa, harin ya afku ne a ranar Juma’a, inda aka kai harin da misalin ƙarfe 1:00 na tsakar dare da wayewar garin ’yan tada ƙayar bayan sun kai hari a kan gadar Azir da kuma runduna ta 25 da ke Damboa.
Majiyoyin sun ce dakarun da ke samun goyon bayan jiragen sama daga rundunar sojin sama, sun yi ta artabu da ’yan ta’addan a wani farmakin da ya ɗauki tsawon sa’o’i biyu ana yi.
“Babban abin da ’yan ta’addan suka sa a gaba shi ne murƙushe birget ɗin soja da ke Damboa, inda suka kai hari ga jama’a, sai dai sojojin sun mayar da martani da ƙarfin wuta, wanda ya yi sanadin jikkatar ‘yan ta’addan da dama,” in ji ɗaya daga cikin majiyoyin.
“Aƙalla gawarwakin ’yan ta’addan 16 ne aka tsinto bayan musayar wuta da aka yi, wasu da dama kuma da ake kyautata zaton sun gudu da raunukan harbin bindiga, sai dai abin takaicin shi ne, sojoji biyu sun rasa ransu a lokacin fafatawar da ’yan ta’addan.
Majiyoyin sun kuma tabbatar da cewa yayin da sojojin suka samu nasarar shawo kan lamarin, fashewar ɗaya daga cikin nakiyoyin ’yan ta’addan ya haddasa gobara a wani wurin ajiyar alburusai, wanda ya yi tasiri ga gine-gine biyu wanda nan take aka shawo kan gobarar.
A halin yanzu ana ci gaba da gudanar da ayyukan zaƙulo ‘yan ta’addan da ke tserewa, yayin da ake ci gaba da gudanar da aikin ceto a kewayen yankin baki ɗaya.
Garin Damboa da ke kudancin Borno, ya sha fuskantar hare-haren ISWAP a lokuta da dama, saboda kyakkyawan wurin da yake.
Sai dai rundunar sojin Najeriyar na ci gaba da fafatawa a yankin domin hana faɗawa hannun ’yan tada ƙayar baya.
Rundunar sojin Operation Haɗin Kai da ke yaƙi da ta’addanci a yankin Arewa maso Gabas, ta ƙara ƙaimi a ’yan makonnin nan, inda ta samu gagarumar nasara a kan mayaƙan ISWAP da ’yan Boko Haram a jihohin Borno da Yobe.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Boko Haram ISWAP yan ta addan
এছাড়াও পড়ুন:
Babban Muftin Oman Ya Yi Suka Kan Taron Kungiyar Larabawa Saboda Rashin Saboda Rashin Ba Wa Gaza Muhimmanci
Babban Mufti na kasar Oman ya bayyana cewa: Matakin taron kungiyar hadin kan kasashen Larabawa ya fi kankara sanyi da rashin muhimmanci
Babban Mufti na masarautar Oman, Sheikh Ahmed bin Hamad Al-Khalili, ya jaddada yabonsa ga fitaccen matsayi na kasar Yemen da kuma matsin lamba da dakarun kasar Yemen suke yi na kai kayan agaji a zirin Gaza. A gefe guda kuma, ya nuna rashin jin dadinsa da raunin kudirin taron kasashen Larabawa kan daukan matakan matsin lamba kan gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila da take aiwatar da kashe-kashen gilla kan al’ummar Falasdinu.
A wani rubutu da ya yi a dandalin X, Al-Khalili ya bayyana godiyarsa ga jaruman kasar Yemen da kuma kasashen da suka bayar da gudumawa wajen matsin lamba don saukaka shigar da kayan agaji Gaza, yana mai cewa, “Ya gode wa Allah da shigar da wasu agajin da aka yi a Gaza,” yana mai jaddada bukatar ci gaba da daukan matakan matsin lamba na kasa da kasa wajen bude mashigar agaji gaba daya.