Sojoji sun kashe mayaƙan ISWAP 16 a Bormo
Published: 23rd, May 2025 GMT
Dakarun sojojin Najeriya na Operation Haɗin Kai da rundunar sojin sama sun daƙile wani harin haɗin gwiwa da ‘yan ta’addar ISWAP suka kai a garin Damboa, inda suka kashe mahara 16 a wani ƙazamin faɗa da suka yi cikin dare.
Mai sharhi kan lamarin tsaro Zagazola Makama ya samu labarin cewa, harin ya afku ne a ranar Juma’a, inda aka kai harin da misalin ƙarfe 1:00 na tsakar dare da wayewar garin ’yan tada ƙayar bayan sun kai hari a kan gadar Azir da kuma runduna ta 25 da ke Damboa.
Majiyoyin sun ce dakarun da ke samun goyon bayan jiragen sama daga rundunar sojin sama, sun yi ta artabu da ’yan ta’addan a wani farmakin da ya ɗauki tsawon sa’o’i biyu ana yi.
“Babban abin da ’yan ta’addan suka sa a gaba shi ne murƙushe birget ɗin soja da ke Damboa, inda suka kai hari ga jama’a, sai dai sojojin sun mayar da martani da ƙarfin wuta, wanda ya yi sanadin jikkatar ‘yan ta’addan da dama,” in ji ɗaya daga cikin majiyoyin.
“Aƙalla gawarwakin ’yan ta’addan 16 ne aka tsinto bayan musayar wuta da aka yi, wasu da dama kuma da ake kyautata zaton sun gudu da raunukan harbin bindiga, sai dai abin takaicin shi ne, sojoji biyu sun rasa ransu a lokacin fafatawar da ’yan ta’addan.
Majiyoyin sun kuma tabbatar da cewa yayin da sojojin suka samu nasarar shawo kan lamarin, fashewar ɗaya daga cikin nakiyoyin ’yan ta’addan ya haddasa gobara a wani wurin ajiyar alburusai, wanda ya yi tasiri ga gine-gine biyu wanda nan take aka shawo kan gobarar.
A halin yanzu ana ci gaba da gudanar da ayyukan zaƙulo ‘yan ta’addan da ke tserewa, yayin da ake ci gaba da gudanar da aikin ceto a kewayen yankin baki ɗaya.
Garin Damboa da ke kudancin Borno, ya sha fuskantar hare-haren ISWAP a lokuta da dama, saboda kyakkyawan wurin da yake.
Sai dai rundunar sojin Najeriyar na ci gaba da fafatawa a yankin domin hana faɗawa hannun ’yan tada ƙayar baya.
Rundunar sojin Operation Haɗin Kai da ke yaƙi da ta’addanci a yankin Arewa maso Gabas, ta ƙara ƙaimi a ’yan makonnin nan, inda ta samu gagarumar nasara a kan mayaƙan ISWAP da ’yan Boko Haram a jihohin Borno da Yobe.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Boko Haram ISWAP yan ta addan
এছাড়াও পড়ুন:
Kungiyar Kare Hakkokin Bil’Adama Ta Siriya Ta Bankado Karin Fararen Hula Da Aka Kashe A Rikicin Suweida
Kungiyar Kare Hakkokin Dan Adam ta Siriya ta bayyana sabbin mutanen da suka mutu sakamakon harin Suweida
Kungiyar kare hakkin dan adam ta Siriya (SOHR) ta bayyana wasu sabbin fararen hula tara da aka ci zarafinsu a lokacin abubuwan da suka faru a Suweida a watan Yulin da ya gabata.
Hukumar da ke sa ido kan lamarin ta bayyana cewa, wadanda aka kashen da suka hada da mata biyu, an kashe su ne a filin wasa a lokacin da wasu ma’aikatun tsaro da na cikin gida na gwamnatin rikon kwarya suke lardin na Suweida, tare da halartar mayakan ‘yan kabilar Larabawan Bedouin.
Hukumar da ke sa ido kan lamarin ta ce adadin mutanen da suka mutu a watan Yulin da ya gabata a tsakanin al’ummar Druze a Suweida ya kai 1,592, yayin da adadin wadanda suka mutu tun safiyar Lahadi 13 ga watan Yuli, sakamakon arangama, da kisa a fili, da kuma harin bama-bamai da sojojin mamayar Isra’ila suka kai ya kai 2,047.
Hukumar da ke sa ido kan lamarin ta yi bayanin cewa, “a ci gaba da bincike, akwai yiyuwar adadin wadanda suka mutu ya karu, ganin cewa akwai wadanda suka bace daga irin wadannan abubuwan da har yanzu ba a tantance makomarsu ba.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Tawagar Yan Wasan Damben Gargajiya Ta Iran Ta Zama Zakara A Damben Ta Duniya September 16, 2025 An Fara Taron Hukumar Makamashin Nukliya Ta Duniya IAEA Karo Na 69 A Birnin Vienna September 16, 2025 Espania Ta Soke Cinikin Makamai Na EUR Miliyon 700 Da HKI Saboda Kissan Kiyashi A Gaza September 16, 2025 Makaman ‘Drons’ Na Yemen Sun Fada Kan Wurare Masu Muhimmanci A HKI September 16, 2025 Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila September 16, 2025 Ministan Tsaron Venezuela Ya Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Juyin Mulki A Kasar September 16, 2025 Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya September 16, 2025 Bayanin Bayan Taron Doha Ya Yi Kira Da A Kafa Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kare Kai September 15, 2025 Fira Ministan Spain: Bai Kamata A Rika Barin “Isr’ila” Tana Shiga Gasar September 15, 2025 Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Sarkin Kasar Qatar A Birnin Doha September 15, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci