Aminiya:
2025-11-03@04:03:12 GMT

Sojoji sun kashe mayaƙan ISWAP 16 a Bormo

Published: 23rd, May 2025 GMT

Dakarun sojojin Najeriya na Operation Haɗin Kai da rundunar sojin sama sun daƙile wani harin haɗin gwiwa da ‘yan ta’addar ISWAP suka kai a garin Damboa, inda suka kashe mahara 16 a wani ƙazamin faɗa da suka yi cikin dare.

Mai sharhi kan lamarin tsaro Zagazola Makama ya samu labarin cewa, harin ya afku ne a ranar Juma’a, inda aka kai harin da misalin ƙarfe 1:00 na tsakar dare da wayewar garin ’yan tada ƙayar bayan sun kai hari a kan gadar Azir da kuma runduna ta 25 da ke Damboa.

An kama jami’in Hukumar NRC da laifin satar waya 2027: ’Yan Najeriya sun yi watsi da takarar Tinubu, sun koka kan tsadar rayuwa

Majiyoyin sun ce dakarun da ke samun goyon bayan jiragen sama daga rundunar sojin sama, sun yi ta artabu da ’yan ta’addan a wani farmakin da ya ɗauki tsawon sa’o’i biyu ana yi.

“Babban abin da ’yan ta’addan suka sa a gaba shi ne murƙushe birget ɗin soja da ke Damboa, inda suka kai hari ga jama’a, sai dai sojojin sun mayar da martani da ƙarfin wuta, wanda ya yi sanadin jikkatar ‘yan ta’addan da dama,” in ji ɗaya daga cikin majiyoyin.

“Aƙalla gawarwakin ’yan ta’addan 16 ne aka tsinto bayan musayar wuta da aka yi, wasu da dama kuma da ake kyautata zaton sun gudu da raunukan harbin bindiga, sai dai abin takaicin shi ne, sojoji biyu sun rasa ransu a lokacin fafatawar da ’yan ta’addan.

Majiyoyin sun kuma tabbatar da cewa yayin da sojojin suka samu nasarar shawo kan lamarin, fashewar ɗaya daga cikin nakiyoyin ’yan ta’addan ya haddasa gobara a wani wurin ajiyar alburusai, wanda ya yi tasiri ga gine-gine biyu wanda nan take aka shawo kan gobarar.

A halin yanzu ana ci gaba da gudanar da ayyukan zaƙulo ‘yan ta’addan da ke tserewa, yayin da ake ci gaba da gudanar da aikin ceto a kewayen yankin baki ɗaya.

Garin Damboa da ke kudancin Borno, ya sha fuskantar hare-haren ISWAP a lokuta da dama, saboda kyakkyawan wurin da yake.

Sai dai rundunar sojin Najeriyar na ci gaba da fafatawa a yankin domin hana faɗawa hannun ’yan tada ƙayar baya.

Rundunar sojin Operation Haɗin Kai da ke yaƙi da ta’addanci a yankin Arewa maso Gabas, ta ƙara ƙaimi a ’yan makonnin nan, inda ta samu gagarumar nasara a kan mayaƙan ISWAP da ’yan Boko Haram a jihohin Borno da Yobe.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram ISWAP yan ta addan

এছাড়াও পড়ুন:

An yi garkuwa da Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Kebbi

’Yan bindiga sun sace Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kebbi, Honarabul Samaila Bagudu, a garinsu da ke Ƙaramar Hukumar Bagudu.

Rahotanni sun bayyana cewa ’yan bindigar sun mamaye garin Bagudu ne da yammacin ranar Juma’a tare da yin harbe-harbe don tsorata al’umma.

Maharan sun yi awon gaba da ɗan majalisar ne a kan hanyarsa ta dawowa daga masallaci bayan ya an idar da sallah masallaci a garin na Bagudu.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Babban Sakataren Yaɗa Labarai na Gwamnatin Jihar Kebbi, Ahmed Idris, ya ce an sanar da hukumomin tsaro, kuma ana ci gaba da ƙoƙarin tabbatar da kuɓutar da Mataimakin Shugaban Majalisar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya
  • Gwamna Uba Sani Ya Bayyana Tsare-tsaren Ci Gaban Kaduna a Taron Duniya a Dubai.
  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • An yi garkuwa da Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Kebbi
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
  • HKI Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza Inda Take Kashe Falasdinawa
  • Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 
  • Shugaban Lebanon Ya Umarci Sojoji Da Su Fuskanci Kutsen Na Isra’ila A Kudancin Kasar
  • Shugaban Lebanon Ya Umarci Sojoji Da Su Fuskanci Duk Wani Kutse Na Isra’ila A Kudancin Kasar