Hamas ta yi tir da kiran da dan majalisar dokokin Amurka ya yi na kai farmakin nukiliya a Gaza
Published: 24th, May 2025 GMT
Kungiyar gwagwarmayar Hamas ta Falasdinu ta yi kakkausar suka kan kalaman baya-bayan nan da dan majalisar dokokin Amurka na jam’iyyar Republican Randy Fine ya yi, wanda ya yi kira da a kai wa zirin Gaza hari da makamin Nukiliya.
Kungiyar Hamas, a cikin wata sanarwa da ta fitar, ta bayyana kalaman dan ‘majalisar a matsayin “laifuffuka” da kuma nuna wariyar launin fata na wasu sassan Amurka.
Kungiyar ta bukaci hukumomin Amurka da na majalisar dokokin kasar da su fito fili su yi Allah-wadai da irin wadannan kalamai.
Hamas ta jaddada cewa furucin dan majalisar Republican na nuni ne karara ta keta dokokin jin kai na kasa da kasa da kuma yarjejeniyar Geneva, kuma yana nufin tunzura kai tsaye don amfani da makaman kare dangi kan fararen hula fiye da miliyan biyu a Gaza.
Kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa (ICC) ta bayar da sammacin kame a watan Nuwamban da ya gabata ga firaministan Isra’ila Netanyahu da tsohon ministan harkokin soji Yoav Gallant, bisa zargin aikata laifukan yaki da cin zarafin bil’adama a Gaza.
Har ila yau Isra’ila na fuskantar shari’ar kisan kiyashi a kotun kasa da kasa kan yakin da ta yi kan yankin gabar tekun da ta yi wa kawanya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Karon farko an tattauna kai tsaye tsakanin ECOWAS da AES
A karon farko an fara tattaunawa tsakanin kungiyar ECOWAS da ta AES ta kawancen kasashen nan guda uku na Sahel da suka balle.
Shugaban hukumar ECOWAS, dan kasar Gambia Omar Touray, ya tattauna a birnin Bamako da ministocin harkokin waje na kasashe mambobin kungiyar AES wato Mali, Burkina da kuma Nijar.
Wannan dai shi ne karon farko tun bayan ficewar kasashen Mali da Burkina Faso da Nijar daga kungiyar ECOWAS a watan Janairun 2024.
Bangarorin sun tattauna kan manyan batutuwan da suka hada da siyasa, diflomasiyya, shari’a, tsaro, da kuma ci gaban tattalin arziki da zamantakewa.
An dai amince, bisa bukatar shugabannin yankin, na kiyaye nasarorin da aka cimma a hadin gwiwar yankin, da tabbatar da zirga-zirgar jama’a da kayayyaki cikin ‘yanci, har zuwa lokacin da aka kulla sabbin yarjejeniyoyin tsakanin ECOWAS da AES.
An kuma yi tsokaci game da bukatar gaggauta yaki da ta’addanci a yayin wannan taro.
Bangarorin biyu sun bayyana damuwarsu kan wannan batu tare da cimma matsaya kan “gaggauta yin aiki don samar da yanayin da ya dace don samar da hadin gwiwa a yaki da ta’addanci.”
Shugaban Hukumar ta ECOWAS da Ministocin Harkokin Waje na Kungiyar ta AES sun amince da ci gaba da yin shawarwarin “kullum bisa bukatu na jama’ar yammacin Afirka.”