Dan majalisar Amurkan mai suna Randall Adam Fine wanda yake wakiltar jam’iyyar “Republican”  ya sake tunanowa duniya  da yadda kasarsa Amurka ta jefa wa biranen Nagasaki da Hiroshima bama-baman Nukiliya a karshen yakin duniya na biyu, ta hanayr yin kira da a jefa wa zirin Gaza irin wadannan makaman na kare dangi.

Kungiyoyin Falasdinawa mabanbanta sun yi tir da wannan irin kira na ci gaba da yi wa Falasdinawa kisan kare dangi, suna masu yin kira ga ita kanta majalisar Amurka da ta fito da yi Allawadai da wannan  kira wanda yake cike da kiyayya.”

Kungiyar Hamas ta bayyana abinda dan majalisar na Amurka ya yi da cewa, ya keta dokokin kasa da kasa da kuma yarjejeniyar Geneva, kamar  kuma yadda yake a matsayin yin kira da a yi wa fiye da fararen hula miliyan daya kisan kiyashi.

Ita kuwa kungiyar jihadul-Islami ta bayyana cewa; Muna daukar kira irin wannan a matsayin yin zuga a fili da a tafka laifi akan bil’adama, sannan kuma abin kunya ne ga ita kanta majalisar Amurka wacce dama sun taba yi wa Bajemine Natanyahu tafi alhali shi ne mafi girman wanda ya tafka laifi aka bil’adama a wannan zamanin.

 A nata bayanin, kungiyar “Popular Front” ta sanar da cewa; Kira irin wannan na a yi wa fararen hula kisan kiyashi b,a shi da banbanci da mafi munin laifukan da ‘yan Nazi su ka tafka.”

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: majalisar Amurka

এছাড়াও পড়ুন:

Arakci Ya Jaddada Muhimmanci Kawo Karshen Yakin Gaza Da Kuma Shigar Da Kayan Agaji

Ministan harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran, Abbas Arakci  wanda ya gana da takwransa na fadar Vatican ya yi kira da a kawo karshen  laifukan  da ‘yan mamaya suke tafkawa akan Gaza da gaggawa a kuma shigar da kayan agaji zuwa yankin.

Ministan harkokin wajen na Iran wanda ya je kasar Italiya domin tattaunawar bayan fage da Amurka akan Shirin kasarsa na Nukiliya, ya ziyarci fadar Vatican, inda ya gana da ministanta na harkokin wajen Cardinal paul Gallagher, ya mika sakon ta’aziyyar rasuwar Fafaroma Farancis sannan kuma da murnar zabar sabon Fafaroma Leo na 14

Abbas Arakci ya yi wa shugabannin fadar ta Vatican bayani akan matsayar Jamhuriyar musulunci ta Iran dangane da shirinta na Nukiliya na zaman lafiya, da kuma inda aka kwana a tattaunawar bayan fage da Amurka.

Haka nan kuma ya yi bayani akan matsayar Iran akan kisan kiyashin da ake yi wa al’ummar Gaza, tare da yin kira da a kawo karshensa da kuma shigar da kayan agaji zuwa yankin.

Haka nan kuma ya yi bayani akan yadda Iran take ganin za a iya warware matsalar mamaya a Falasdinu da ita ce yin kuri’ar raba gardaga da dukkanin Falasdinawa,musulmi kiristoci da yahudawa za su shiga  a ckin tsarin demokradiyya.

A karshe bangarorin biyu sun jaddada muhimmanci tattaunawa a tsakanin addinai domin shimfida sulhu da zaman lafiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Arakci Ya Jaddada Muhimmanci Kawo Karshen Yakin Gaza Da Kuma Shigar Da Kayan Agaji
  • Kungiyar Ta’addanci Ta ISIS Ta Zargi Shugaban Gwamnatin Siriya Da Kauce Hanya Madaidaiciya
  • Yan Majalisar Tarayya Na Katsina Sun Mara Wa Gwamna Dikko Radda Baya Don Takarar Zango Na Biyu
  • Wani Dan Majalisar Dokokin Kasar Amurka Ya Bukaci Amurka Ta Jefa Makaman Nukliya Kan Gaza
  • Mayar Da Hankali A Aikin Farfado Da Kwararrun Asibitocin Gwamnatin Tarayyya
  • Ƙungiyar ’yan Majalisar Dokokin Ƙasa Ta APC Ta Amince Da Takarar Tinubu A Zaɓen 2027 
  • MDD ta yi gargadin cewa jarirai 14,000 a Gaza kan iya mutuwa idan an ci gaba da killace Zirin 
  • Sin Ta Soki Yunkurin Amurka Na Hana Amfani Da Chips Kirar Kasar Sin
  • Majalisar Wakilai Za Ta Gabatar Da Dokoki Biyar Don Gyara Bangaren Man Fetur