Gwamnatin Sudan Ta Yi Allah Wadai Da Sabbin Takunkuman Da Amurka Ta Kakaba Mata
Published: 25th, May 2025 GMT
Gwamnatin Sudan ta bayyana cewa: Sabbin takunkuman da Amurka ta kakaba mata, bakar siyasa ce ta nemen bata mata suna
A cikin wata sanarwa da gwamnatin Sudan ta fitar, ta yi Allah-wadai da matakin da gwamnatin Amurka ta dauka na kakaba mata sabbin takunkumai, tana mai bayyana hakan a matsayin maimaita kura-kurai irin na baya kan yadda gwamnatocin Amurka suka tafiyar da harkokin Sudan cikin kura-kurai.
Sanarwar ta kara da cewa: “takunkuman da Amurka ta fitar, zarge-zarge ne da suke neman bata sunan kasar da murguda gaskiyar lamari; inda ta ci gaba da bayyana cewa: “Amurka tana ci gaba da bin manufofin da ke kawo cikas ga hanyar da al’ummar Sudan ke bi wajen samun kwanciyar hankali da zaman lafiya.”
Gwamnatin Sudan ta jaddada cewa: “Takunkuman da Amurka ta kakaba wa sojojin ne bayan nasarorin da suka samu a fagen yaki da suka hada da sauya gaskiyar yakin.”
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Allah Ya yi wa Malam Nata’ala rasuwa
Allah Ya yi wa fitaccen jarumin Kannywood, Mato Na Mato, wanda aka fi sani da Malam Nata’ala a cikin shirin Dadin Kowa rasuwa.
Wannan na cikin wani saƙo da fitacciyar marubuciya, Fauziyya D. Sulaiman ta wallafa a shafinta na Facebook a daren ranar Lahadi.