Kungiyar ta’addanci ta Da’ish ko ISIS ta zargi shugaban gwamantin kasar Siriya al-Julani da yin sujjada a kofar shiga wajen kafirai

Kungiyar ta’addanci ta Da’ish ko ISIS ta bayyana shugaban sabuwar gwamnatin Siriya Abu Muhammad al-Julani a matsayin azzalumi wanda ya sayar da addininsa tare da yin sujjada a kofar shiga wajen kafirai.

Ta yi kira ga ‘yan kasashen waje da ke cikin jami’an tsaron Siriya da su tuba su yi watsi da hidimar da suke yi wa azzalumi.

A cikin wani sako na addini, a kokarinta na jan hankali masu saurarenta wadanda ta kira su “masu hijira saboda Allah,” kungiyar ta’addanci ta ISIS ta fitar da wani kira na farfaganda ga wasu ‘yan kasashen waje da kuma sabbin hukumomin tsaro na gwamnatin Siriya, kungiyar ISIS ta yi kira ga ‘yan kasashen waje da ke kasar Siriya da su tuba su daina yi wa sabon shugaban gwamnatin Siriya Abu Muhammad al-Julani biyayya da hidima, wanda ta bayyana shi a matsayin azzalumin da ya sayar da addininsa tare da yin sujada a kofar mashigar kafirai.

Sakon kungiyar ta ISIS na kunshe da gargadi mai tsanani ga wadanda ke ci gaba da aiki a cikin sabuwar gwamnatin Siriya. Har ila yau, sakon ya hada da barazanar kai hare-haren soji, da nuna kasancewar mambobinta da ta tura su zuwa yankunan karkara, tare da yin barazanar mayar da martani ga duk wani mataki da aka dauka kanta.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: gwamnatin Siriya

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

 

Wata sanarwa da Daraktan Yada Labarai da Hulda da Jama’a na Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya, Folasade Boriowo, ya fitar, ta ce a karon farko cikin shekaru da dama, daliban Nijeriya za su ci gaba da karatun tarihin Nijeriya tun daga Firamare 1 zuwa karamar Sakandare 3 yayin da daliban SSS 1 – 3 za su koyi sabon darasin da aka samar na ‘Civic and Heritage Studies’, wanda ya hada tarihin Nijeriya da Ilimin zamantakewar Jama’a.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
  • Hamas Ta Karyata Gwamnatin Mamayar Isra’ila Kan Shirga Karya Don Kare Muggan Manufofinta
  • Kwamitin bincike na MDD ya zargi Isra’ila da aikata “kisan kare dangi” a Gaza
  • Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
  • Kungiyar Kare Hakkokin Bil’Adama Ta Siriya Ta Bankado Karin Fararen Hula Da Aka Kashe A Rikicin Suweida
  • Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya tare da kiyaye hadin kai
  • Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar
  • Gwamnatin Sudan Ta Ce: Babu Sulhu Da ‘Yan Tawayen Kasar Na Kungiyar Rapid Support Forces
  • Kasashen Larabawa da na Musulmi na taron gaggawa kan harin Isra’ila a Qatar