Dole Ne A Bai Wa Al’umma Damar Mallakar Kananan Makamai Domin Kare Kansu – Shugaban DSS
Published: 14th, February 2025 GMT
“Ba wai kawai sun fatattake su ba ne, sun kwace makamansu, kuma tun a wancan lokacin, har yanzu, zai yi wuya ka ji wani labarin mahara a Tafawa Balewa, don haka, shawo kan kalubalen tsaro, dole sai an saka duk wasu masu ruwa da tsaki a cikin lamarin.
“Tsammanin sojojin Nijeriya, ‘yansanda, ko DSS, za su kare kowane dan Nijeriya ko kowace gwamnati, Hakan ba zai yi wu ba,” in ji shi.
Ajayi ya kara da cewa, dole ne kasar ta samar da matakan tsaro domin rage nauyi a kan tushen tsare-tsaren tsaron kasa.
এছাড়াও পড়ুন:
2027: Ba Mu Kafa Haɗakarmu Don Cika Burin Atiku Ba – ADC
Abdullahi ya ce tun kafin a kafa haɗakar, wasu sun riga sun fara yaɗa cewa an shirya ta ne domin Atiku.
Ya ƙara da cewa: “Ni ina da shekara 56, wa ya ce ba zan iya tsayawa takarar shugaban ƙasa ba?”
Da aka tambaye shi game da Peter Obi, tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar LP, Abdullahi ya ce Obi na cikin haɗakar har yanzu.
Amma ya ce bai zama cikakken ɗan jam’iyyar ADC ba har yanzu.
Ya bayyana cewa jam’iyyar ADC ta bai wa Obi da kuma tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, dama su fice daga jam’iyyunsu na yanzu wato LP da SDP.
Ya kuma ce Obi ba zai koma jam’iyyar PDP ba, duk da cewa jam’iyyar tana ƙoƙarin jawo ‘yan siyasa domin dawo da ƙarfinta.
Da aka tambaye shi dalilin da ya sa ‘yan Nijeriya za su yadda da jam’iyyarsu, Abdullahi ya ce jam’iyyar APC da ke mulki ta yi alƙawarin kawo sauyi amma ta gaza.
Don haka, ya ce lokaci ya yi da ‘yan Nijeriya za su gwada wata sabuwar tafiyar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp