Babbar Kotun Tarayya da ke Jihar Kano, ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a S.M. Shuaibu ta ƙi amincewa da buƙatar wasu mambobin Kwamitin Musabaƙar Alƙur’ani da ke son a hana EFCC bincike kan yadda aka sayar da wani fili mai darajar Naira biliyan 3.5.

Filin da ake magana a kai yana bayan titin Ahmadu Bello Way, kuma yana da faɗin hekta biyu.

Sojoji sun kashe mayaƙan ISWAP 16 a Borno An kama jami’in Hukumar NRC da laifin satar waya

Tsohon Gwamnan Sojan Kano, Kanal Abdullahi Wase ne, ya bayar da filin don a gina katafaren waje da za a riƙa gudanar da musabaƙar Alƙur’ani duk shekara.

Amma daga baya sai wasu mambobin kwamitin suka ga an gina gidaje 38 a filin ba tare da sanin su ba.

Hakan ne ya sa a ranar 11 ga watan Nuwamba, 2023, wasu daga cikin amintattun kwamitin suka kai wa EFCC ƙara, domin ta binciki yadda aka sayar da filin a ɓoye.

Waɗanda suka shigar da ƙarar sun haɗa da Sheikh Ibrahim Shehu Mai Hula, Sheikh Gwani Yahuza Danzarga, Tijjani Bala Kalarawi, Aliyu Harazimi, Barrister Saidu Koki, Ado Shehu Maibargo, Dokta Aliyu Darma, Tijjani Mai Lafiya Sanka, Alhaji Tukur Gadanya da Alhaji Sabiu Bako.

Sun buƙaci kotu ta hana EFCC gayyatarsu ko cafke su dangane da wannan batu, sun dogar da wasu sashe na kundin tsarin mulki da yarjejeniyar kare haƙƙin ɗan adam ta Afirka.

Amma kotu ta ce EFCC na da hurumin gudanar da bincike kamar yadda doka ta tanadar, kuma babu kotun da za ta hana hakan, musamman idan ana zargin aikata laifi.

Don haka, kotu ta bayyana cewa waɗana ake ƙara su biya Naira 250,000 ga waɗanda suka yi ƙararsu, saboda ɓata musu lokaci.

Lauyoyin da suka kare wanda ake ƙara – Sadiq Yahya da John Chukwu Eze – sun yaba da hukuncin kotun, yayin da lauyan masu ƙara, Yahaya Isa Abdulrasheed, ya ce za su ɗaukaka ƙara.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Wasu Yahudawa Sun Hana Kayakin Agaji Shiga Yankin Gaza

Bayan watannin kimani biyu da rabi wanda gwamnatin HKI suka hana kayakin abinci da magunguna shiga yankin zirin Gaza, a jiya talata, gwamnatin Natanyahu ta bada damar a shigo da wasu kadan da kayakin agajin, saboda takurawar wasu shuwagabnni a kasashen yamma.

Amma duk da haka a yau wasu yahudawa fararen hula sun hana wucewar wata mota makare da abinci shigowa zirin gaza daga kofar shiga yankin ta Karen Abu Salem.

Hotunan bidiyo sun nuna yadda jerin gwanon motoci dauke da kayakin agaji zuwa gaza amma wasu yahudawa dauke da tutocin HKI sun zo sun tsaya a gaban daya daga cikinsu suna fadar cewa basu yarda a shigar da kayakin agaji zuwa gaza ba har sai sun mutu gaba daya.

 Sannan a dayan bangaren kuma sojojin HKI rike da bindigogi sun zuba masu ido suna kallo.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kotu A Iraki Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Tsohon Jami’in Kasar Kan Hannu A Kashe-Kashen Rayukan Jama’a
  • Dakarun Yemen Sun Hana Zirga-Zirgan Jiragen Sama A Filin Jirgin Saman Ben Gurion Na Isra’ila
  • Kotu Ta Yanke Wa Mutum 5 Hukuncin Ɗaurin Wata 1 Saboda Awakinsu Sun Cinye Bishiyar Gwamnati A Kano
  • Kotu Ta Yanke Hukunci Wa Mutum 5 Ɗaurin Wata 1 Saboda Awakinsu Sun Cinye Bishiyar Gwamnati A Kano
  • Kotu Ta Soke Umarnin Kwace Filin Asibitin Tiamin, Ta Umarci Gwamnatin Kano Ta Biya Diyyar ₦2.6bn
  • Kotu Ta Soke Umarnin Kwace Filin Asibitin Tiamin, Ta Umarci Gwamnatin Kano Ta Biya Diyyar Biliyan ₦2.6bn
  • Zargin Satar Fasaha: Kotu ta sanya ranar yanke hukunci kan shari’ar BBC
  • Hukumar tace fina-finai ta soke lasisin gidajen gala 8 a Kano
  • Wasu Yahudawa Sun Hana Kayakin Agaji Shiga Yankin Gaza