Gwamnatin Gombe za ta taimaki ’yar shekara 14 da aka yi wa auren dole
Published: 25th, May 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Gombe, na shirin taimaka wa wata yarinya ’yar shekara 14 da aka tilasta yi mata auren dole a Jihar Taraba.
Kwamishinar Ma’aikatar Mata da Walwala, Asma’u Iganus, ta ce yarinyar ta nemi taimako bayan da kakanta ya ɗaura mata aure da wani mutum a matsayin mata ta huɗu.
An kama Hakimi kan zargin taimaka wa ’yan bindiga a Neja Jami’an Sibil Difens sun bude wuta a garin JosTa ce hakan ya ci zarafin yarinyar kuma gwamnati ba za ta zuba ido ba.
“Mun fara ɗaukar matakan kare ta. Mun tuntuɓi kotu kuma lauyoyin gwamnati za su shiga shari’ar don kare ta,” in ji Asma’u.
Ta ce yarinyar ta ce tana son ci gaba da karatu, don haka gwamnati za ta saka ta a cikin tsarin shirin AGILE domin ta koma makaranta.
Haka kuma an ba ta tallafin kuɗi, abinci da kayan amfani don rage mata wahalhalu.
Lauyar Ma’aikatar Shari’a, Barista Marilyn Na’omi Abdu, ta ce za su yi iya ƙoƙari wajen kare yarinyar a kotu.
Yarinyar ta ce asalin ta daga Gombe ta ke, amma suna zaune a Taraba inda mahaifinta ke noma.
Ta ce kakanta ya tilasta yi mata auren wani mutum mai kuɗi ba tare da amincewarta ba.
“Ina zaune kawai sai aka ce an ɗaura min aure. Ban san shi ba kuma bana son shi,” in ji ta.
Ta ce mijin yana azabar da ita, har ɗaure ta yake da ƙarfi kafi kafin ya sadu da ita.
Ta nuna yadda ya ji mata ciwo a hannunta a matsayin shaida da irin dukan da ta ke sha.
Daga ƙarshe, ta gudu zuwa Gombe don neman taimako.
Gwamnatin Gombe, ta ce za ta ci gaba da kare yara mata da faɗakar da jama’a kan illar auren dole.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: gwamnati Taraba yarinya
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
Daga Usman Muhammad Zaria
Majalisar Zartarwa ta Jihar Jigawa ta amince da bayar da rancen kudi ga hukumar gidaje ta jihar domin gina gidaje 52 a Dutse.
A cikin wata sanarwa da kwamishinan yada labarai na jihar, Alhaji Sagir Musa Ahmed ya fitar, ya bayyana cewa gidajen za su kunshi masu dakuna uku da kuma dakuna biyu kowanne.
Ya ce aikin zai kasance a gaban tsohuwar unguwar majalisar dokoki, kusa da hanyar wucewa ta Jami’ar Tarayya da je Dutse, a matsayin wani shiri na asusun gina gidaje karkashin ma’aikatar gidaje, ci gaban birane da tsare-tsaren yankuna, ta hannun hukumar gidaje ta jihar.
Alhaji Sagir ya bayyana cewa, wannan mataki na nuna kudirin gwamnati wajen magance matsalar gidaje a babban birnin jihar, kara habaka ci gaban birane, tare da samar da ayyukan yi ga matasan jihar.
Ya ce an tsara wannan asusu ne domin tabbatar da dorewa, ta yadda za a ci gaba da zuba jari a ayyukan samar da gidaje masu araha a fadin jihar.
Haka kuma ya kara da cewa, gwamnatin jihar tana da kudirin ci gaba da inganta rayuwar al’ummarta, ta hanyar ayyuka masu amfani da jama’a, da ke inganta walwala, karfafa tattalin arziki, da tallafa wa matasa.
Kwamishinan ya kuma bayyana cewa, majalisar ta amince da bayar da kwangilar gyara da inganta gidan baki guda biyu (Malam Adamu Chiroma House da kuma Senator Francis Ella House) da ke cikin G9 Quarters a Dutse, da kudin sama da naira miliyan 219.7.
Ya ce aikin zai haɗa da cikakken gyara da inganta gine-ginen, gyaran hanyoyin ruwa da kuma girka tankokin ruwa ga kowanne daga cikin gidajen biyu.
Ya ce hakan na da nufin tabbatar da wadataccen ruwan sha mai dorewa a wuraren.
Alhaji Sagir Musa Ahmed ya kara da cewa, amincewar da aka yi da wannan kwangila na nuna jajircewar gwamnatin jihar wajen kula da dukiyar jama’a da kuma tabbatar da cewa gine-ginen gwamnati suna cikin yanayi mai kyau da nagarta.