Gwamnatin Gombe za ta taimaki ’yar shekara 14 da aka yi wa auren dole
Published: 25th, May 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Gombe, na shirin taimaka wa wata yarinya ’yar shekara 14 da aka tilasta yi mata auren dole a Jihar Taraba.
Kwamishinar Ma’aikatar Mata da Walwala, Asma’u Iganus, ta ce yarinyar ta nemi taimako bayan da kakanta ya ɗaura mata aure da wani mutum a matsayin mata ta huɗu.
An kama Hakimi kan zargin taimaka wa ’yan bindiga a Neja Jami’an Sibil Difens sun bude wuta a garin JosTa ce hakan ya ci zarafin yarinyar kuma gwamnati ba za ta zuba ido ba.
“Mun fara ɗaukar matakan kare ta. Mun tuntuɓi kotu kuma lauyoyin gwamnati za su shiga shari’ar don kare ta,” in ji Asma’u.
Ta ce yarinyar ta ce tana son ci gaba da karatu, don haka gwamnati za ta saka ta a cikin tsarin shirin AGILE domin ta koma makaranta.
Haka kuma an ba ta tallafin kuɗi, abinci da kayan amfani don rage mata wahalhalu.
Lauyar Ma’aikatar Shari’a, Barista Marilyn Na’omi Abdu, ta ce za su yi iya ƙoƙari wajen kare yarinyar a kotu.
Yarinyar ta ce asalin ta daga Gombe ta ke, amma suna zaune a Taraba inda mahaifinta ke noma.
Ta ce kakanta ya tilasta yi mata auren wani mutum mai kuɗi ba tare da amincewarta ba.
“Ina zaune kawai sai aka ce an ɗaura min aure. Ban san shi ba kuma bana son shi,” in ji ta.
Ta ce mijin yana azabar da ita, har ɗaure ta yake da ƙarfi kafi kafin ya sadu da ita.
Ta nuna yadda ya ji mata ciwo a hannunta a matsayin shaida da irin dukan da ta ke sha.
Daga ƙarshe, ta gudu zuwa Gombe don neman taimako.
Gwamnatin Gombe, ta ce za ta ci gaba da kare yara mata da faɗakar da jama’a kan illar auren dole.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: gwamnati Taraba yarinya
এছাড়াও পড়ুন:
Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Yace Mutanen Kasarsa Suna Cikin Shiri Don Kare Kansu Da Karfi
Ministan harkokin wajen kasar Aran Abbas arachi ya bayyana cewa mutanen kasarsa a shirin suke su ci gaba da kare kasarsu daga Amurka da kuma HKI .
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Abbas Aragchi yana fadar haka a jiya litinin a lokacinda yake ganawa da tawagar kasar Brazil a gefen taron kungiyar BRICS karo 17 wanda ke tafiya a halin yanzu a birnin Rio de Jenero na kasar Brazil.
An gudanar da wannan taron ne saboda hare-haren da HKI da kuma Amurka suka kaiwa JMI a baya bayan nan, da kuma tasirinsa a cikin al-amuran siyasa da kuma tattalin arziki a yankin Asiya ta yamma da kuma duniya gaba daya.
Abbas Aragchi ya bayyana cewa hare-haren HKI da kuma Amurka ya sabawa dikokin kasa da kasa sannan ko wane bangare yana da rawar da zai take don ganin an tabbatar da zaman lafiya a duniya.
A nashi bangaren ministan harkokin wajen kasar Rasha Sergey Lavrov yace: hare-hare kan kasar Iran musamman a kan shirinta na makamashin nukliya na zaman lafiya abin yin tir da shi ne. Sannan ya kara da cewa kasar Rasha a shirye take ta taimaka ko a fagen kwamitin tsaro na MDD ne.