Aminiya:
2025-07-10@13:36:01 GMT

Gwamnatin Gombe za ta taimaki ’yar shekara 14 da aka yi wa auren dole

Published: 25th, May 2025 GMT

Gwamnatin Jihar Gombe, na shirin taimaka wa wata yarinya ’yar shekara 14 da aka tilasta yi mata auren dole a Jihar Taraba.

Kwamishinar Ma’aikatar Mata da Walwala, Asma’u Iganus, ta ce yarinyar ta nemi taimako bayan da kakanta ya ɗaura mata aure da wani mutum a matsayin mata ta huɗu.

An kama Hakimi kan zargin taimaka wa ’yan bindiga a Neja Jami’an Sibil Difens sun bude wuta a garin Jos

Ta ce hakan ya ci zarafin yarinyar kuma gwamnati ba za ta zuba ido ba.

“Mun fara ɗaukar matakan kare ta. Mun tuntuɓi kotu kuma lauyoyin gwamnati za su shiga shari’ar don kare ta,” in ji Asma’u.

Ta ce yarinyar ta ce tana son ci gaba da karatu, don haka gwamnati za ta saka ta a cikin tsarin shirin AGILE domin ta koma makaranta.

Haka kuma an ba ta tallafin kuɗi, abinci da kayan amfani don rage mata wahalhalu.

Lauyar Ma’aikatar Shari’a, Barista Marilyn Na’omi Abdu, ta ce za su yi iya ƙoƙari wajen kare yarinyar a kotu.

Yarinyar ta ce asalin ta daga Gombe ta ke, amma suna zaune a Taraba inda mahaifinta ke noma.

Ta ce kakanta ya tilasta yi mata auren wani mutum mai kuɗi ba tare da amincewarta ba.

“Ina zaune kawai sai aka ce an ɗaura min aure. Ban san shi ba kuma bana son shi,” in ji ta.

Ta ce mijin yana azabar da ita, har ɗaure ta yake da ƙarfi kafi kafin ya sadu da ita.

Ta nuna yadda ya ji mata ciwo a hannunta a matsayin shaida da irin dukan da ta ke sha.

Daga ƙarshe, ta gudu zuwa Gombe don neman taimako.

Gwamnatin Gombe, ta ce za ta ci gaba da kare yara mata da faɗakar da jama’a kan illar auren dole.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gwamnati Taraba yarinya

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Za Ta Yi Nazarin Sabuwar Gayyatar Da Amurka Ta Yi Mata Na  Sabuwar Tattaunawa

Ma’aikatar harkokin wajen Iran ta sanar da cewa, tana nazarin sabuwar gayyatar da Amurka ta yi mana na komawa teburin tattaunawa.

 Kamfanin dillancin labarun “Mehr” na Iran ya nakalto wata majiya mai karfi tana cewa, bayan da Amurka ta kasa dakatar da Shirin kasar na makamashin Nukiliya, ta aiko ma ta da takardar gayyata domin yin zama da ita akan teburin tattaunawa.

Majiyar ma’aikatar harkokin wajen Iran ta fada wa kamfanin dillancin labrun “Mehr” cewa, Amurka ta aiko da sakwanni ta hanyar ‘yan aike na kasashe masu yawa.”

Ma’aikatar harkokin wajen ta Jamhuriyar musulunci ta Iran tana yin nazari akan hakikanin abinda Amurkan take so, da kuma yadda tattaunawar za ta kasance wacce za ta zama ta dage takunkumai, da kuma darajar uranium din da Iran za ta tace, sannan kuma da biyanta…  na barnar da aka yi mata sanadiyyar kallafaffen yaki.

Tun da dari, Amurka ta yi kokarin nuna cewa Iran ce ta bukaci ayi tatttaunawar, lamarin da Jamhuriyar musulunci ta Iran ta kore.

Ministan harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran Abbas Akarci, ya sha bayyana cewa, duk wata tattaunawa idan har za a yi ta, to za ya kasance ne akan manufar kare maslahar jamhuriyar musulunci ta Iran. Batun ci gaba da tace nadarin uranium kuwa, wani abu wanda Iran ba za ta taba ja da baya a kansa ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwamandan Sojin Iran Ya Jaddada Kare Kan Iyakokin Jamhuriyar Musulunci Ta Iran
  • Babban Kwamandan Sojin Iran Ya Bayyana Cewa Iran Ta Koyawa Gwamnatin Isra’ila Hankali
  • HKI: Sojoji 62 Ne Su Ka Halaka A Gaza A Cikin Wannan Shekara Ta 2025
  • 2027: Idan ADC na son lashe zaɓe dole ta bai wa ɗan Arewa takara — Okonkwo
  • Gamayyar ‘Yan Adawa Sun Kaddamar ADC A Gombe  
  • An ƙayyade maki da shekarun shiga jami’a a Nijeriya
  • Iran Za Ta Yi Nazarin Sabuwar Gayyatar Da Amurka Ta Yi Mata Na  Sabuwar Tattaunawa
  • Mata Da Matasa Dari Hudu Suka Amfana Da Tallafi A Gandun Albasa Kano
  • Dalilin da matan karkara a Kano suka fi son haihuwa a gida
  • Bidiyon tsiraici: Babiana ta sake jawo ce-ce-ku-ce