Kotu A Iraki Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Tsohon Jami’in Kasar Kan Hannu A Kashe-Kashen Rayukan Jama’a
Published: 23rd, May 2025 GMT
Kotun kolin kasar Iraki ta yanke hukuncin kisa kan wani tsohon jami’in gwamnatin kasar kan laifin aikata kisa da kuma boye gawarwakinsu
Kotun kolin kasar Iraki ta yanke hukuncin kisa a jiya Alhamis kan wani tsohon jami’in gwamnatin kasar kan laifin aikata kisan gilla da kishe-kashe kan ‘yan kasar da kuma boye gawarwakinsu a manyan kaburbura.
A cikin wata sanarwa da majalisar koli ta shari’ar kasar Iraki ta fitar ta bayyana cewa: Kotun kolin manyan laifuka ta kasar Iraki ta yanke hukuncin kisa kan daya daga cikin jiga-jigan tsohuwar gwamnatin kasar Khairallah Hammadi Abd Jaru bisa laifin aikata kisan gillar da aka yi wa mutane 198 daga yankin Balad a shekara ta 1981, da kuma hannu a cikin aiwatar da hukuncin kisa kan ‘yan kasar da kuma boye gawarwakinsu a cikin manyan kaburbura.
Sanarwar kotun kolin ta kara da cewa: Mai laifin ya taba rike mukamin daraktan tsaron kasar kuma ya rike mukamai da dama a wasu lardunan kasar kafin shekarar 2003.
Sanarwar ta kuma bayyana cewa: Wanda ake tuhumar ya shiga cikin kama jama’a da aiwatar da kashe-kashe kansu a gundumar Balad bisa zarginsu da kasancewa ‘yan jam’iyyar Da’awa mai alaka da addinin Musulunci, baya ga gano manyan kaburbura, da aka kashe jama’a a lokacin shugabancinsa a larduna.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Iraki ta
এছাড়াও পড়ুন:
An Kaddamar Da Shirin Samar Da Wutar Lantarki A Jami’ar Kashere Gombe.
Shugaban kasa Bola Tinubu ya ce gwamnatin tarayya za ta gudanar da aikin samar da wutar lantarki ga jami’ar tarayya ta Kashere da ke jihar Gombe domin tabbatar da samar da isasshen wutar lantarki domin inganta harkokin ilimi.
Shugaban ya bayyana hakan ne a wajen taron hadaka karo na uku na jami’ar tarayya ta Kashere da ke karamar hukumar Akko a jihar Gombe.
Shugaba Bola Tinubu ya kuma bayyana cewa ma’aikatar albarkatun ruwa ta tarayya za ta fara aikin gina madatsar ruwa a kogin Kashere domin tallafa wa shirin koyar da aikin gona na jami’ar da inganta samar da ruwa ga al’ummomin da ke kewaye.
Ya jaddada kudirin gwamnatinsa na inganta samar da ingantaccen ilimi ta hanyar shiga tsakani na asusun bayar da lamuni na ilimi na kasa (NELFUND).
Ya kuma bukaci jami’o’in Najeriya da su binciko tsarin samar da kudade mai ɗorewa yana mai cewa dole ne zamanin dogaro da kai ga ayyukan gwamnati ya ba da dama ga sabbin hanyoyin samar da kudaden shiga, da haɗin gwiwar dabarun bunƙasa dukiyoyi da kuma asusun bayar da tallafi na gari.
A jawabinsa na maraba, Shugaban jami’ar tarayya ta Kashere, farfesa Umar Pate, ya bayyana cewa martabar jami’ar tana karuwa ne saboda shekaru masu yawa na tsare-tsare da hangen nesa na Hukumar gudanarwar jami’ar.
Ya ce cibiyar ta ba da fifikon dacewa da ilimi ta hanyar ingantaccen ayyukan bincike da haɗin gwiwa tare da sahihan cibiyoyi na ƙasa da ƙasa.
HUDU Shehu