Kotu A Iraki Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Tsohon Jami’in Kasar Kan Hannu A Kashe-Kashen Rayukan Jama’a
Published: 23rd, May 2025 GMT
Kotun kolin kasar Iraki ta yanke hukuncin kisa kan wani tsohon jami’in gwamnatin kasar kan laifin aikata kisa da kuma boye gawarwakinsu
Kotun kolin kasar Iraki ta yanke hukuncin kisa a jiya Alhamis kan wani tsohon jami’in gwamnatin kasar kan laifin aikata kisan gilla da kishe-kashe kan ‘yan kasar da kuma boye gawarwakinsu a manyan kaburbura.
A cikin wata sanarwa da majalisar koli ta shari’ar kasar Iraki ta fitar ta bayyana cewa: Kotun kolin manyan laifuka ta kasar Iraki ta yanke hukuncin kisa kan daya daga cikin jiga-jigan tsohuwar gwamnatin kasar Khairallah Hammadi Abd Jaru bisa laifin aikata kisan gillar da aka yi wa mutane 198 daga yankin Balad a shekara ta 1981, da kuma hannu a cikin aiwatar da hukuncin kisa kan ‘yan kasar da kuma boye gawarwakinsu a cikin manyan kaburbura.
Sanarwar kotun kolin ta kara da cewa: Mai laifin ya taba rike mukamin daraktan tsaron kasar kuma ya rike mukamai da dama a wasu lardunan kasar kafin shekarar 2003.
Sanarwar ta kuma bayyana cewa: Wanda ake tuhumar ya shiga cikin kama jama’a da aiwatar da kashe-kashe kansu a gundumar Balad bisa zarginsu da kasancewa ‘yan jam’iyyar Da’awa mai alaka da addinin Musulunci, baya ga gano manyan kaburbura, da aka kashe jama’a a lokacin shugabancinsa a larduna.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Iraki ta
এছাড়াও পড়ুন:
Wani Dan Majalisar Dokokin Kasar Amurka Ya Bukaci Amurka Ta Jefa Makaman Nukliya Kan Gaza
Wani dan majalisar dokokin kasar Amurka daga jam’iyyar Republican daga jihar Florida Randi Fine ya bukaci gwamnatin Amurka ta yi amfani da dimbin makaman N uklkiya da ta tara don kawo karshen yaki a gaza, ta kashe dukkan Falasdinawa a lokaci guda a huta.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Fine yana fadar haka a wata hira da ta hadashi da tashar talabijin ta Foxnews a jiya Alhamis.
Ya kuma kara da cewa Amurka bata shiga tattaunawa da sojojin Nazi a yakin dunbiya na biyu ba, bata kuma yi kome bas ai da ta yi amfani da makaman nuklioya a kan Hiroshima da kuma Nagasafi sai kasar Japan ta mika kai ba tare da wasu matsala ba.
Fine yace a yanzun ma al-amarin ya kai ga zabin amfani da Nukliya kan Gaza kawai ta rage.
Labarin ya kara da cewa wannan bas hi ne karon farko wanda Randy Fine yake kiran gwamnatin Amurka ta yi haka ba. Kuma ya sha suka daga kungiyoyi daban daban.