Daga Bello Wakili

Dukkan ‘yan majalisun tarayya daga Jihar Katsina sun bayyana goyon bayansu ga Gwamna Umar Dikko Radda domin ya sake tsayawa takara a wa’adin mulki na biyu karkashin jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a zaben shekarar 2027 mai zuwa.

An bayyana wannan matsaya ne a lokacin wani taron hadin gwiwa da ‘yan majalisar suka gudanar, inda Honourable Sada Soli, dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Jibia da Kaita, ya yi magana a madadin takwarorinsa.

Ya bayyana cewa wannan shawara ta samo asali ne daga nazarin hadin gwiwa da suka yi kan nasarorin da gwamnan ya samu da kuma goyon bayan da al’ummar jihar suka nuna daga kowane bangare.

‘Yan majalisar sun yaba da irin salon shugabanci na Gwamna Radda, inda suka bayyana shi a matsayin shugaba mai hangen nesa da kuma wanda ke tafiyar da mulki cikin hadin kai.

Sun jaddada cewa gwamnatinsa ta samu gagarumin ci gaba wajen yaki da rashin tsaro, sauya fasalin ilimi, bunkasa noma, karfafa tattalin arziki da kuma karfafa al’umma.

A cewarsu, wadannan kokari sun sanya Jihar Katsina ta fara tafiya kan turbar ci gaba mai dorewa da walwala.

Don karfafa wannan matsaya, Sanata Abdulaziz Yar’adua mai wakiltar mazabar Katsina ta Tsakiya, ya goyi bayan kudirin a madadin sauran sanatoci biyu daga jihar.

Ya ce su ma sanatocin sun amince da matsayar da ‘yan majalisar wakilai suka dauka, tare da bayyana Gwamna Radda a matsayin dan takarar gwamna daya tilo na jam’iyyar APC a zaben 2027.

‘Yan majalisar sun yi alkawarin bayar da cikakken goyon baya da aminci ga yunkurin gwamnan na sake tsayawa takara, tare da kira ga dukkan ’ya’yan jihar Katsina da su hade kai domin ci gaba da tafiya a hanya daya ta dorewar cigaba da hadin kai.

Wannan hadin kai daga bangarorin majalisar wakilai da ta dattijai na nuna karuwar karfin siyasa ga Gwamna Radda yayin da zaben 2027 ke karatowa.

COV/BELLO WAKILI 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Yan majalisa Goyon Baya Mara Baya Takarar yan majalisar

এছাড়াও পড়ুন:

Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC

Za a gudanar da kwarya-kwaryan taron shugabannin kungiyar APEC karo na 32 a Koriya ta Kudu.

Eduardo Pedrosa, babban daraktan sakatariyar APEC, ya bayyana cewa tun bayan shigarta APEC, Sin ta kasance mamba mai himma da kwazo. Kuma a halin yanzu, tana taka muhimmiyar rawa wajen ba da jagoranci a karkashin tsarin APEC, haka kuma tana mai da hankali kan yadda za a inganta samar da manyan ci gaba a yankin da kuma duniya baki daya.

Eduardo Pedrosa ya bayyana haka ne kwanan nan yayin wata hira da babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na Sin wato CMG a birnin Gyeongju dake Koriya ta Kudu. Ya kuma yaba da nasarorin da Sin ta samu a tafarkinta na zamanantar da kanta.(Safiyah Ma)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Kasar Sin Ce Ke Da Sama Da Rabin Muhimman Makaloli Na Duniya October 30, 2025 Daga Birnin Sin Bunkasar Fannin Kirkire-Kirkiren Fasahohi Na Sin Alheri Ne Ga Dukkanin Duniya Ba Barazana Ba October 30, 2025 Daga Birnin Sin Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21 October 30, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya
  • Gwamna Uba Sani Ya Bayyana Tsare-tsaren Ci Gaban Kaduna a Taron Duniya a Dubai.
  • An yi garkuwa da Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Kebbi
  • Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC
  • Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda
  • Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP
  • An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara
  • Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC
  • Majalisa ta amince Tinubu ya karɓo rancen dala biliyan 2.35
  • Zargin Kisan Kiristoci: ’Yan majalisar Amurka sun yi amfani da bayanai marasa tushe — Gwamnati