Yan Majalisar Tarayya Na Katsina Sun Mara Wa Gwamna Dikko Radda Baya Don Takarar Zango Na Biyu
Published: 23rd, May 2025 GMT
Daga Bello Wakili
Dukkan ‘yan majalisun tarayya daga Jihar Katsina sun bayyana goyon bayansu ga Gwamna Umar Dikko Radda domin ya sake tsayawa takara a wa’adin mulki na biyu karkashin jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a zaben shekarar 2027 mai zuwa.
An bayyana wannan matsaya ne a lokacin wani taron hadin gwiwa da ‘yan majalisar suka gudanar, inda Honourable Sada Soli, dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Jibia da Kaita, ya yi magana a madadin takwarorinsa.
Ya bayyana cewa wannan shawara ta samo asali ne daga nazarin hadin gwiwa da suka yi kan nasarorin da gwamnan ya samu da kuma goyon bayan da al’ummar jihar suka nuna daga kowane bangare.
‘Yan majalisar sun yaba da irin salon shugabanci na Gwamna Radda, inda suka bayyana shi a matsayin shugaba mai hangen nesa da kuma wanda ke tafiyar da mulki cikin hadin kai.
Sun jaddada cewa gwamnatinsa ta samu gagarumin ci gaba wajen yaki da rashin tsaro, sauya fasalin ilimi, bunkasa noma, karfafa tattalin arziki da kuma karfafa al’umma.
A cewarsu, wadannan kokari sun sanya Jihar Katsina ta fara tafiya kan turbar ci gaba mai dorewa da walwala.
Don karfafa wannan matsaya, Sanata Abdulaziz Yar’adua mai wakiltar mazabar Katsina ta Tsakiya, ya goyi bayan kudirin a madadin sauran sanatoci biyu daga jihar.
Ya ce su ma sanatocin sun amince da matsayar da ‘yan majalisar wakilai suka dauka, tare da bayyana Gwamna Radda a matsayin dan takarar gwamna daya tilo na jam’iyyar APC a zaben 2027.
‘Yan majalisar sun yi alkawarin bayar da cikakken goyon baya da aminci ga yunkurin gwamnan na sake tsayawa takara, tare da kira ga dukkan ’ya’yan jihar Katsina da su hade kai domin ci gaba da tafiya a hanya daya ta dorewar cigaba da hadin kai.
Wannan hadin kai daga bangarorin majalisar wakilai da ta dattijai na nuna karuwar karfin siyasa ga Gwamna Radda yayin da zaben 2027 ke karatowa.
COV/BELLO WAKILI
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Yan majalisa Goyon Baya Mara Baya Takarar yan majalisar
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu Zai Bibiyi Kwazon Ministocinsa A Ranar 29 Ga Watan Mayu
“Idan ka yi kwao sosai, babu abin da za ka ji tsoro. Idan ba ka yi kwazo ba, za mu biyiya. Idan ba ka yi komai ba, za ka bar mana aikinmu,” in ji shugaban kasa.
Masu ruwa da tsaki sun ce wasu ministoci, musamman a cikin muhimman sassa, suna cikin bincike yayin da Tinubu ke shirin yanke hukunci a kan inganta majalisar ministocinsa.
A yanzu dai ana zuba ido a gani ko dai Tinubu zai gudanar da sauye-sauye a majalisar ministocinsa cikin gaggawa ko kuma zai jinkinta.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp