Firaministan Sin Ya Sauka A Indonesia Domin Ziyarar Aiki
Published: 25th, May 2025 GMT
A yau Asabar ne firaministan kasar Sin Li Qiang, ya sauka a birnin Jakarta domin ziyarar aiki a kasar Indonesia bisa gayyatar da shugaban kasar Indonesia Prabowo Subianto ya yi masa.
Li ya bayyana cewa, kasashen Sin da Indonesia sun bayar da misali kan yadda manyan kasashe masu tasowa suke aiki tare don kara karfi da cin moriyar juna da kuma samun nasara ga kowane bangare.
Ya ce, kasar Sin a shirye take ta yi aiki tare da Indonesia don ci gaba da samar da wadata ga al’ummomin Sin da Indonesia ta hanyar tabbatar da makoma guda a tare, da bin hanyar zamanantarwa.
Kazalika, ya ce, a matsayinsu na manyan kasashe masu tasowa, kuma manyan muhimman kasashe masu karfi a cikin kasashe masu tasowa, ya kamata Sin da Indonesia, su ci gaba da raya ruhin Bandung zuwa mataki na gaba, da karfafa hadin kai da daidaita lamurra, da kuma kara matse kaimi ga tabbatar da aiki da hakikanin tsarin damawa da kasashe daban daban. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Ma’aikatan Wutar Lantarki A Katsina Sun Tsunduma Yajin Aiki
Ya kuma ce suna sane da cewa yajin aikin zai iya shafar jama’a musamman a Katsina.
“Ba ma’aikata kaɗai muke ba – iyaye ne mu kuma masu ciyar da iyali. Abin da muke nema kawai haƙƙinmu ne,” in ji shi.
Yajin aikin zai iya haifar da tsaiko wajen samun wutar lantarki a yankin, musamman a Katsina inda yajin aikin ke da zafi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp