An kama yarinya kan kashe jariri a sansanin ’yan gudun hijira
Published: 23rd, May 2025 GMT
Rundunar ’yan sandan Jihar Borno ta kama wata yarinya ’yar shekara 15 bisa zargin jefa gawar wani jariri a cikin wani banɗaki da ke sansanin ’yan gudun hijira a Monguno.
A cewar wata majiyar ’yan sanda a ranar 22 ga Mayu, 2025, da misalin ƙarfe 9:15 na safe, an bayar da rahoton cewa, a safiyar wannan rana da misalin ƙarfe 6:00 na safe, an tsinci gawar wani jariri da aka haifa a yashe a ɗaya daga cikin banɗaki da ke sansanin.
Majiyar ta ce, wacce ake zargin mai suna Yafalmata Alhaji Mustapha mai shekara 15, da ke da zama a sansanin, a yanzu haka tana hannun ’yan sanda domin bincike.
“‘Yan sanda da ƙwararrun likitoci sun ziyarci wurin kuma an kai gawar jaririn zuwa babban asibitin Monguno. Likitan ya tabbatar da mutuwar jaririn da isarsa, kuma an ajiye gawar a asibiti domin a duba.” in ji majiyar.
Bayan binciken gawar an miwa ta ga shugaban sansanin ‘yan gudun hijira na Charamari domin yi masa jana’iza kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Gudun Hijra
এছাড়াও পড়ুন:
Mutanen unguwa sun kama masu ƙwacen waya a Kano
Al’ummar yankin Bachirawa a Jihar Kano sun yi ta maza sun cafke wasu matasa biyu da ake zargi da ƙwace waya a unguwar a yayin da ɓata-garin suke tsaka da ƙwacen.
Matasan dai sun tare wata mata ce a unguwar suka ƙwace mata waya, wanda hakan ya sa mutanen yankin suka yi kansu tare da kama su.
An samu nasarar karɓe wayar da suka amsa tare da ƙwace makaman da aka samu a hannunsu.
Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ne ya sanar da haka bayan al’ummar sun miƙa waɗannan matasa ofishin ’yan sanda a ranar Juma’a.