Aminiya:
2025-05-24@00:17:27 GMT

An kama yarinya kan kashe jariri a sansanin ’yan gudun hijira

Published: 23rd, May 2025 GMT

Rundunar ’yan sandan Jihar Borno ta kama wata yarinya ’yar shekara 15 bisa zargin jefa gawar wani jariri a cikin wani banɗaki da ke sansanin ’yan gudun hijira a Monguno.

A cewar wata majiyar ’yan sanda a ranar 22 ga Mayu, 2025, da misalin ƙarfe 9:15 na safe, an bayar da rahoton cewa, a safiyar wannan rana da misalin ƙarfe 6:00 na safe, an tsinci gawar wani jariri da aka haifa a yashe a ɗaya daga cikin banɗaki da ke sansanin.

Kotu ta bai wa EFCC izinin binciken sayar da filin musabaƙar Alƙur’ani na N3.5bn a Kano Sojoji sun kashe mayaƙan ISWAP 16 a Borno

Majiyar ta ce, wacce ake zargin mai suna Yafalmata Alhaji Mustapha mai shekara 15, da ke da zama a sansanin, a yanzu haka tana hannun ’yan sanda domin bincike.

“‘Yan sanda da ƙwararrun likitoci sun ziyarci wurin kuma an kai gawar jaririn zuwa babban asibitin Monguno. Likitan ya tabbatar da mutuwar jaririn da isarsa, kuma an ajiye gawar a asibiti domin a duba.” in ji majiyar.

Bayan binciken gawar an miwa ta ga shugaban sansanin ‘yan gudun hijira na Charamari domin yi masa jana’iza kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Gudun Hijra

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnan Filato Ya Kafa Kwamiti Don Binciken Hare-Haren Da Ake Kai Wa A Jihar

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Cutar lamoniya ta kama alhazai 99 ’yan ƙasar Indonesiya a Saudiyya
  •  MDD Ta Nuna Damuwa Akan Tabarbarewar Yanayin “Yan Hijira A Gabashin  Kasar Chadi
  • An kama wani matashi da ya yi shigar mata a Adamawa
  • Wani Mutum Ya Harbe Ma’aikatan Ofishin Jakadancin Isra’ila A Birnin Washington Na Amurka
  • Araghchi: Iran ba za ta tattauna kan batun inganta sinadarin Uranium din ta ba
  • Sojojin HKI Sun Bude Wuta Kan Jami’an Diblomasiyyar Wadanda Suka Je Jenin
  • ‘Yansanda Sun Kama Matasa 2 Da Ake Zargi Da Satar Mota A Kebbi
  • Gwamnan Filato Ya Kafa Kwamiti Don Binciken Hare-Haren Da Ake Kai Wa A Jihar
  • Wani Mutum Ya Kashe Matarsa Da Duka Har Lahira A Edo