Tsokaci Kan Yadda Wasu Matasa Ke Yin Aure Ba Tare Da Sana’a Ba
Published: 24th, May 2025 GMT
Abin da ma yake faruwa kenan yanzu wallahi matasan nan maza! namiji babu sana’a babu isasshen ilimin zamani ke wallahi na addini ma wani babu sai ya tattago aure ko da yake an ce adashi suke shiga da an dauka sai zancen kai kudi karshe dai abar iyaye da wahala shi ya sa auren ma baya cin Litinin da Laraba an watse.
Sunana Lubabatu Auta Ingawa:
A gaskiya akwai kuskure me girma da kuma da-na-sanin da yake biyo bayan yin aure babu sana’a da kuma karancin ilimi. Babban kalubalen shi ne; rashin iya sauke nauyin duk wata dawainiya ta matar saboda babu wata sana’a ko aikin yi ga mijin da kudi zai iya shigo masa. Matasa masu son aure ina baku shawara ku tabbatar da kuna da abin yi wanda zai iya rike gida dan gudun je-ka-nayi-ka, idan an taru an yi maka aure ba fa za a taru wajen rika maka mata ba. Sannan ina kira ga iyaye su jajirce wajen ganin ‘ya’yansu sun samu ayyukan yi ko sana’o’i da kasuwanci kafin aure. Ke ma da za a aura kada ki bari soyayya ta debe ki, ki amince da auren ci-ma-zaune, wallahi idan ta kakare mafitar kawai shi ne saki, ki dawo gida ki zama karamar bazawara. A rika hakuri da jiran lokaci da tunani me kyau kafin aiwatar da komai na rayuwa.
Sunana Murjanatu Nasir daga Naija:
Wannan kuskure ne babba daukowa kai aure ba tare da sana’a ba, ina ganin kokarin masu yin hakan, na gaishe ku ‘yan kunar bakin wake, wannan ai sakawa kai damuwa da kuma nemawa kai rashin kwanciyar hankali ne bayan an yi aure. Dalilai na kuwa su ne; muddin aka yi aure tun kan soyayya ta kare za a fara fuskantar matsaloli da kalubalen da aka ja wa kai, rashin abubuwa zai yi sallama sakamakon masu taimakawar sun fara gajiya to, babu sana’a sai roko, karantun ma wani ba yadda ba a yi ba ya samu ya karasa ko takaddunsa ya ajjiye watarana a dace amma mutum ya ki sabida zuciya ta afka tafkin kogin soyayya. Roko zai yawaita yayin da ta haihu roko zai ci gaba, kai ne nan, gobe kai ne can kullum cikin roko, tun ana baka har a daina bakai, wani in ya ji tausayinka ya ce ka kawo takaddunka ya sama maka aiki nan ma babu su, har girma ya zo karfi ya kare.
Sunana Hassana Sulaiman Hadejia A Jihar Jigawa:
Wasu daga cikin matasan abin da ke sa su yi hakan shi ne gasa da take shiga tsakaninsu na cewa wane yayi ni ma ko ta ya sai nayi auren. Kuskuren da yake tsakaninsu matasan da kuma su kansu iyayen shi ne rashin tunanin mai hakan zai iya janyo wa gaba, kawai suna yanke hukuncin cewa idan aka yi Allah ne zai hore. Tabbas akwai matsalolin da za su iya zuwa gaba kamar; rashin zaman lafiya da samun nutsawa cikin zamantakewar auren kansa, da yawaitar samun matsalolin da za su iya haifar da rabuwar auren kansa. Yin aure da kyakkyawar sana’a yana haifar da gobe mai kyau ga zamantakewar aure, da kuma hasashen samun nutsawa da samar da tarbiyyar yara idan an samu. Shawarar da ya kamata kowanne bangare ya dauka a nan shi ne; Auren lokaci ne kuma idan yayi kowa zai yi kawai dai ana dan zurfafa tunani kafin yin nasa.
Sunana Muhammad Isah Zareku Miga A Jahar Jigawa:
A gaskiyar magana wasu matasan sukan bijirowa kansu aure alhalin basu da halin yi amma kuma ni a ganina laifin iyayen su ne saboda a karkara ma iyayen su ne suke daure musu gindi tunda ciyarwar ma iyayen su ne suke yi ba wai matasan ba. Haka zalika dukka buyin suna kuskure mai makon a daurewa matashi gindi yayi sana’a ko karatu mai zurfi sai kawai daya fara tasawa sai ayi masa aure kuma dole ana samun rabuwar aure barkatai saboda bashi da ilimin auren. Akwai matsala ana samun rabuwar aure barkatai, ma’auratan basa samun jittuwa. Amfani yin aure da kwakkawar sana’a shi ne matshin zai iya rike matar da duk wata dawainiyar ta tazaman aure. Shawarar ita ce matashi ya dage da neman sana a da kuma ilimin sannan iyayen su ma suna nusar da yaransu akan neman sana’a da kuma ilimin.
Sunana Fatima Nura Kila A Jihar Jigawa:
Tabbas hakan babban kuskurene a gare mu yin aure ba sana’a, ya kamata mu matasa mu nutsu mu san me muke yi domin matukar ba sana’a aka yi aure, auren ba inda zai je zai rabu saboda babu kulawa ta fannin addininmu daya tanadar. A wannan bangaren gaskiya daga matan har mazan ba ma kan daidai akan wannnan abun, domin kuwa sana’a babbar jigo ce daga mazan har matan. Tabbas akwai sun hada da; Yawan tunani, zaman banza, saurin fushi, sata da sauransu. Tabbas amfanin shi ne; samun nutsuwa da cikar buri da kuma samun lafiya. Ya kamata mu matasa mu tashi mu nemin sana’a idan muka tsaya da kafafunmu sai mu yi aure domin bahaushe ya ce babu maraya sai rago. Iyaye kuma su ci gaba da tsayawa akan ‘ya’yansu wajen ganin sun inganta rayuwar ‘ya’yansu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Limamin Masallacin Jumma’a A Nan Tehran Ya Yi Magana Dangane Da Kwatar Garin Khurramshar Daga Sojojin Sadam
Mataimakin limamin Jumma’a a nan Tehran Sheikh kum Hujjatul Islam Kazen Sadiki bayan yayio Magana a kan al-amuran tsaron All..da kuma yadda bayin All..da kuma shidanun mutane zasu mutu da kuma yadda sakamakon ko wannansu a gaban All…/ Ya kuma ya gamanar fatahin garin KharramShahr dake kudancin kasar Iran kuma kan iyaka da kasar Iran, wanda dakarun kare juyin juya halin musulunci tare da sauran sojoji da mayakan sa kai suka kwace wannan garin daga hannun sojojin Sdam Hussain a rana irin ta yau wato 2 ga watan Khordod.
Banda haka lamamin yana Magana kan littafan da aka buga dangane da wannan gagarumin fatahin da mutanen Iran suka sami a kan wannan garin. Wanda kuma daga wannan nasarar ne ta ci gaba da samun nasara har aka kawo karshen yakin a shekara 1988M.