Abin da ma yake faruwa kenan yanzu wallahi matasan nan maza! namiji babu sana’a babu isasshen ilimin zamani ke wallahi na addini ma wani babu sai ya tattago aure ko da yake an ce adashi suke shiga da an dauka sai zancen kai kudi karshe dai abar iyaye da wahala shi ya sa auren ma baya cin Litinin da Laraba an watse.

Abin cewa nan yaro dai ya nutsu ya nemi sana’a da zai dogara da kansa sannan ya iya daukar nauyin iyali kuma a nemi karatu bakin iyawa. Su iyaye suna gujewa yaro abin da zai je ya zo ne ka dauko ‘yar mutane babu sana’a za a ci soyayya ne ina kai ba karatu ba sai kame-kame wani lokacin ma su iyaye su yaro yake bari da wahala a ci da shi a ci da matarsa, in Allah ya kawo rabo haka za a yi ta kin an haihu ko rigar jariri ba a siya ba. To, duk namijin da yake da kwakkwarar sana’a ai shi ne namijin aure babu rashin ci bale rashin sha da sutura, ya yi wa kansa ya yi wa iyali ya yi wa iyayen bakidaya.

 

Sunana Lubabatu Auta Ingawa:

A gaskiya akwai kuskure me girma da kuma da-na-sanin da yake biyo bayan yin aure babu sana’a da kuma karancin ilimi. Babban kalubalen shi ne; rashin iya sauke nauyin duk wata dawainiya ta matar saboda babu wata sana’a ko aikin yi ga mijin da kudi zai iya shigo masa. Matasa masu son aure ina baku shawara ku tabbatar da kuna da abin yi wanda zai iya rike gida dan gudun je-ka-nayi-ka, idan an taru an yi maka aure ba fa za a taru wajen rika maka mata ba. Sannan ina kira ga iyaye su jajirce wajen ganin ‘ya’yansu sun samu ayyukan yi ko sana’o’i da kasuwanci kafin aure. Ke ma da za a aura kada ki bari soyayya ta debe ki, ki amince da auren ci-ma-zaune, wallahi idan ta kakare mafitar kawai shi ne saki, ki dawo gida ki zama karamar bazawara. A rika hakuri da jiran lokaci da tunani me kyau kafin aiwatar da komai na rayuwa.

 

Sunana Murjanatu Nasir daga Naija:

Wannan kuskure ne babba daukowa kai aure ba tare da sana’a ba, ina ganin kokarin masu yin hakan, na gaishe ku ‘yan kunar bakin wake, wannan ai sakawa kai damuwa da kuma nemawa kai rashin kwanciyar hankali ne bayan an yi aure. Dalilai na kuwa su ne; muddin aka yi aure tun kan soyayya ta kare za a fara fuskantar matsaloli da kalubalen da aka ja wa kai, rashin abubuwa zai yi sallama sakamakon masu taimakawar sun fara gajiya to, babu sana’a sai roko, karantun ma wani ba yadda ba a yi ba ya samu ya karasa ko takaddunsa ya ajjiye watarana a dace amma mutum ya ki sabida zuciya ta afka tafkin kogin soyayya. Roko zai yawaita yayin da ta haihu roko zai ci gaba, kai ne nan, gobe kai ne can kullum cikin roko, tun ana baka har a daina bakai, wani in ya ji tausayinka ya ce ka kawo takaddunka ya sama maka aiki nan ma babu su, har girma ya zo karfi ya kare.

 

Sunana Hassana Sulaiman Hadejia A Jihar Jigawa:

Wasu daga cikin matasan abin da ke sa su yi hakan shi ne gasa da take shiga tsakaninsu na cewa wane yayi ni ma ko ta ya sai nayi auren. Kuskuren da yake tsakaninsu matasan da kuma su kansu iyayen shi ne rashin tunanin mai hakan zai iya janyo wa gaba, kawai suna yanke hukuncin cewa idan aka yi Allah ne zai hore. Tabbas akwai matsalolin da za su iya zuwa gaba kamar; rashin zaman lafiya da samun nutsawa cikin zamantakewar auren kansa, da yawaitar samun matsalolin da za su iya haifar da rabuwar auren kansa. Yin aure da kyakkyawar sana’a yana haifar da gobe mai kyau ga zamantakewar aure, da kuma hasashen samun nutsawa da samar da tarbiyyar yara idan an samu. Shawarar da ya kamata kowanne bangare ya dauka a nan shi ne; Auren lokaci ne kuma idan yayi kowa zai yi kawai dai ana dan zurfafa tunani kafin yin nasa.

 

Sunana Muhammad Isah Zareku Miga A Jahar Jigawa:

A gaskiyar magana wasu matasan sukan bijirowa kansu aure alhalin basu da halin yi amma kuma ni a ganina laifin iyayen su ne saboda a karkara ma iyayen su ne suke daure musu gindi tunda ciyarwar ma iyayen su ne suke yi ba wai matasan ba. Haka zalika dukka buyin suna kuskure mai makon a daurewa matashi gindi yayi sana’a ko karatu mai zurfi sai kawai daya fara tasawa sai ayi masa aure kuma dole ana samun rabuwar aure barkatai saboda bashi da ilimin auren. Akwai matsala ana samun rabuwar aure barkatai, ma’auratan basa samun jittuwa. Amfani yin aure da kwakkawar sana’a shi ne matshin zai iya rike matar da duk wata dawainiyar ta tazaman aure. Shawarar ita ce matashi ya dage da neman sana a da kuma ilimin sannan iyayen su ma suna nusar da yaransu akan neman sana’a da kuma ilimin.

 

Sunana Fatima Nura Kila A Jihar Jigawa:

Tabbas hakan babban kuskurene a gare mu yin aure ba sana’a, ya kamata mu matasa mu nutsu mu san me muke yi domin matukar ba sana’a aka yi aure, auren ba inda zai je zai rabu saboda babu kulawa ta fannin addininmu daya tanadar. A wannan bangaren gaskiya daga matan har mazan ba ma kan daidai akan wannnan abun, domin kuwa sana’a babbar jigo ce daga mazan har matan. Tabbas akwai sun hada da; Yawan tunani, zaman banza, saurin fushi, sata da sauransu. Tabbas amfanin shi ne; samun nutsuwa da cikar buri da kuma samun lafiya. Ya kamata mu matasa mu tashi mu nemin sana’a idan muka tsaya da kafafunmu sai mu yi aure domin bahaushe ya ce babu maraya sai rago. Iyaye kuma su ci gaba da tsayawa akan ‘ya’yansu wajen ganin sun inganta rayuwar ‘ya’yansu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Manoma a Jigawa Sun Jinjinwa Kungiyar Sasakawa Africa Bisa Bada Tallafi a Harkar Noma

Daga Usman Muhammad Zaria

 

Kananan manoma a jihar Jigawa sun yabawa kungiyar Sasakawa Africa dangane da tallafin da take samarwa a fannin inganta noma.

Yayin tattaunawa da wasu daga cikin wadanda suka ci moriyar shirin musamman manoman shinkafa a garin Chandam dake karamar hukumar Birnin Kudu, sun bayyana cewa tallafin Sasakawa ya habaka noman shinkafar su tare da samun karin kudade.

Manoman sun bayyana cewar shirin ya taimaka masu wajen bunkasa harkokin noma tare da tallafawa al’ummomin su.

Daya daga cikin wadanda suka amfana da shirin a yankin Chandam dake karamar hukumar Birnin Kudu, Buhari Nafi’u, yace Sassakawa Africa ta samar masu da tallafin  noma daban daban.

A cewar sa tallafin sun hada da horo wanda ya taimakawa kananan manoma wajen ganin sun kara samun kudade tare da inganta rayuwar maza da mata a yankin.

Yace a wannan shekarar sun noma amfanin gona mai yawa sakamakon horon da suka samu karkashin shirin, inda suka hadu sukayi noman a kungiyance a yankin Birnin Kudu.

Buhari ya kara da cewar, a shekarun baya suna daukan kwanaki casa’in kafin su girbe shinkafa amma zuwan Sassakawa ya sa sun yi noma tare da girbe amfanin gonan su a cikin kwanaki saba’in saboda irin da kungiyar ta basu.

Yace yanzu haka sun fara amfani da shinkafar da suka noma a gidajen su.

Yace an basu takin zamani kyauta tare da sauran kayayyakin feshi.

Ya godewa tallafin na Sassakawa, yana mai cewar zai cigaba da amfani da irin da aka basu tare da koyar da mazauna yankin abubuwan da aka horar da su akai.

Shi ma Malam Rufai Nasiru daga yankin na Chandam  yace sun kara samun ilimi akan sabbin dubarun noma wanda suka samu daga kungiyar ta Sassakawa.

Yace a bana ya noma buhun shinkafa 8 ba kamar a baya ba da yake noma buhu biyar, yana mai cewa shirin yana da inganci kuma zai cigaba da amfani da irin da kungiyar ta basu.

A garin Chuwasu  dake karamar hukumar Taura, Aminu Babanyara ya bayyana cewar sun ci moriyar shirin ta hanyar samun iri masu inganci da takin zamani da kuma horo akan sabbin dubarun noma.

Yace wasu daga cikin abubuwan da suka koya sun hada da amfani da shara wajen yin taki a gida inda suka ce hakan yasa sun samu karin shinkafa da geron da suke nomawa idan aka kwatanta da shekarun baya.

Babanyara, yace sabbin dubarun da suka koya da kuma irin da Sassakawa suka basu, ya basu damar ninka abin da suka saba nomawa a damina sau uku.

Yace da farko suna da shakku akan amfani  da sabbin irin da sabbin dubarun noman, amma kuma bayan sun gwada a shekaru biyu na farko sun ga alfanun hakan wajen bunkasa amfanin gonan da suke nomawa.

Manoman sun kuma yi kira ga kunyiyar ta Sassakawa ta samar masu da injinan casa domin saukaka masu al’amura.

Malama Amina Abdulrahman wacce tayi jawabi a madadin kungiyar mata manoma a Karamar  Hukumar Taura, tace shirin tallafin Sassakawa ya kawo sauyi a rayuwar su musamman a fannin samun kasuwanci da amfanin gonar da ake sarrafawa don yin abinci mai gina jiki na yara.

A cewar ta an horar da su akan yadda za su samar da abinci mai gina jiki a yankuna tare da yadda za su yi aiki a kungiyance don inganta noma.

A don haka, tayi kira ga kungiyar Sassakawa ta samar masu da injinan sarrafa amfanin gona na zamani.

Yankunan da aka ziyarta sun hada da Chandan dake Birnin Kudu da kuma Sabon Gari shi ma a karamar hukumar Birnin Kudu.

Sauran sun hada da Baranda dake Dutse da kuma Chuwasu dake karamar hukumar Taura.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Matar aure ta yanka wuyan mijinta, ta fasa masa ido da wuƙa a Neja
  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka
  • IAEA : Babu wata shaida da ke nuna cewa Iran na kera makaman nukiliya
  • Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon
  • Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
  • Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace
  • Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba
  • Manoma a Jigawa Sun Jinjinwa Kungiyar Sasakawa Africa Bisa Bada Tallafi a Harkar Noma
  • Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar